Kalamai masu ratsa zuciya da Zahra Buhari tayi ga mijinta a cikarsu shekaru 4 da aure

Kalamai masu ratsa zuciya da Zahra Buhari tayi ga mijinta a cikarsu shekaru 4 da aure

- Zahra Buhari, diyar shugaban kasa Muhammadu Buhari ta wallafa cikar aurenta shekaru 4 da mijinta

- Ta yi wallafar ne a shafinta na kafar sada zumuntar zamani ta Instagram, inda ta bayyana soyayyarta ga mijinta

- A cewar Zahra, da Ahmed Indimi zai kara bukatar aurenta a karo na biyu, da ta kara amincewa

Zahra Buhari Indimi da mijinta Ahmed Indimi suna shagalin cikar aurensu shekaru 4 cur.

Zahra ta wallafa kalami masu nuna kaunarta ga mijinta, da fatan cigaba da rayuwa dashi a rayuwa a shafinta na kafar sada zumuntar zamani na Instagram.

Kamar yadda Zahra ta wallafa: "Idan har akwai bukatar in kara aurenka, tabbas da na kara.

"Barka da zagayowar shekarun aurenmu 4, @ahmed.indimi, rayuwata ba za ta taba zama daidai ba idan da babu kai.

"Ya Allah, ka sanya ma'aurata su zama sanyin idanuwan juna. Ameen ya Wadud."

Kalamai masu ratsa zuciya da Zahra Buhari tayi ga mijinta a cikarsu shekaru 4 da aure
Kalamai masu ratsa zuciya da Zahra Buhari tayi ga mijinta a cikarsu shekaru 4 da aure. Hoto daga mrs_zmbi
Asali: Instagram

KU KARANTA: Ban taba shiga bakin cikin rayuwa kamar haka ba, Matar da aka sace danta da jikanta a Kankara

KU KARANTA: Iyakokin kasar nan da ke bude ke assasa rashin tsaro, Kwamitin arewa

A wani labari na daban, tsohon gwamnan jihar Zamfara, Sani Yarima, ya bayyana burinsa na tsayawa takarar shugaban kasa a 2023, a karkashin jam'iyyar APC, Daily Trust ta wallafa hakan.

Yarima, sanata mai wakiltar Zamfara ta yamma a majalisar tarayya, ya sanar da manema labarai kudirinsa a ranar Laraba a Abuja, inda yace yana son ya samu nasara don ya gyara rayuwar 'yan Najeriya ne.

Tsohon gwamnan ya bayyana tsananin takaicin da ya shiga bayan ganin yadda ake kashe-kashe a kasar nan duk da bakar fatara da talaucin da ke addabar 'yan Najeriya.

Yarima yace: "Idan ba a manta ba, a 2006, na bayyana kudirina na burin zama shugaban kasar Najeriya, bayan na mulki jihar Zamfara na shekaru 8."

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel