Yanzu-yanzu: Gwamna Matawalle ya kulle makarantun Zamfara dake makwabtaka da Katsina da Kaduna

Yanzu-yanzu: Gwamna Matawalle ya kulle makarantun Zamfara dake makwabtaka da Katsina da Kaduna

- Gwamnatin Zamfara ta rufe makarantu goma a jihar don gudun abinda ya faru a Katsina

- Daga cikin makarantun nan akwai na kwana da kuma na jeka da dawo

- Kwamishanan ilmin jihar ya bayyanawa manema labarai dalilin hakan

Labarin dake shigowa da duminsa na nuna cewa gwamnatin jihar Zamfara ta bada umurnin kulle dukkan makarantun jihar dake makwabtaka da jihohin Katsina da Kaduna.

TVC ta ruwaito cewa gwamnatin ta tabbatarwa iyayen daliban makarantun dake cikin Gusau da ba'a kulle ba cewa kada su damu akwai isasshen tsaro a cikin gari.

Yanzu-yanzu: Gwamna Matawalle ya kulle makarantun Zamfara dake makwabtaka da Katsina da Sokoto
Yanzu-yanzu: Gwamna Matawalle ya kulle makarantun Zamfara dake makwabtaka da Katsina da Sokoto
Asali: Twitter

DUBA NAN: Hazikan soji sun damke 'yan fashi da masu taimaka musu a Zamfara

Kwamishanan ilmin jihar Zamfara, Ibrahim Abdullahi, ya bayyana cewa ma'aikatarsa ta baiwa gwamnan shawaran rufe wadannan makarantu gudun kada a faru da jihasr Katsina ya afka musu.

Yace: "A nan jihar Zamfara muna kokarin kiyaye faruwan abinda ya faru a Kankara."

"Saboda haka mun baiwa gwamna shawara ya rufe wasu makarantun kwana dake iyaka da jihar Kaduna da jihar Katsina."

"Ba dukkan makarantun kwana dake Zamfara aka rufe ba."

Ga jerin makarantun da gwamnatin jihar ta rufe:

GASS Zurmi

GSS Birnin Magaji

GSSS Bayumkafi

GSS Ape

GSSS Bokuyum

GSSS Dan Sadau

GDSS Nasarawa Malayi

GDSS Gusami

GDSS Gudun Kore

GDSS Tsafe

KU DUBA: Majalisar dattawa ta aika sammaci ga ministan tsaro da shugabannin tsaro kan satar daliban Kankara

Mun kawo muku cewa kungiyar Boko Haram ta sanar da cewa ita ce keda alhakin sace dalibai fiye da 300 daga makarantar sakandiren kimiyya da ke Kankara a jihar Katsina, kamar yadda HumAngle ta rawaito.

A cewar HumAngle, shugaban kungiyar Boko Haram, Abubakar Shekau, ya ce har yanzu basu tuntubi kowa dangane da wasu sharuda na sakin daliban ba.

Jaridar ta ce, Shekau ya sanar da hakan ne a cikin wani sakon sautin murya mai tsawon mintuna 4:28 da ya fitar da duku-dukun safiyar ranar Talata.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Kalli bidiyin channels:

Asali: Legit.ng

Online view pixel