Yanzu-yanzu: Gwamnan jihar Legas, Babajide Sanwo Olu ya shiga killace kansa

Yanzu-yanzu: Gwamnan jihar Legas, Babajide Sanwo Olu ya shiga killace kansa

- Bayan wata da watanni yana yaki da cutar Korona a jiharsa, gwamnan Legas ya killace kansa

- Da yiwuwan cutar Korona ta dawo kwashe mutane yayinda mutane 3000 suka kamu cikin watan Disamba

Gwamnan jihar Legas, Babajide Sanwo-Olu, zai shiga killace kansa, bayan daya daga cikin hadimansa na jiki ya kamu da cutar Korona ranar Alhamis.

Za'a yiwa gwamna Sanwo-Olu da mambobin majalisarsa gwajin cutar Korona ranar Juma'a amma zai cigaba da killace kansa kar lokacin da sakamakon ya fito.

"Muna fuskantar hauhawar adadin masu kamuwa da cutar COvID-19 a jihar Legas kuma dukkan al'ummar jihar su bi ka'idojin baiwa juna tazara, tsaftace hannu da kuma gujewa taron jama'a," kwamishanan lafiyan jihar, Akin Abayomi yace.

A cewar Abayomi, wannan ba shi bane kare na farko da za'a yiwa gwamnan Legas gwajin COVID-19.

KU DUBA: Kamfanin Atiku, INTELS, ya kori ma'akata 700, ya hanasu hakkinsu

Yanzu-yanzu: Gwamnan jihar Legas, Babajide Sanwo Olu ya shiga killace kansa
Yanzu-yanzu: Gwamnan jihar Legas, Babajide Sanwo Olu ya shiga killace kansa
Asali: Twitter

KU KARANTA: Najeriya ta samu adadin sabbin masu cutar Coronavirus 675 ranar Alhamis

A bangare guda, gwamnatin tarayya a ranar Alhamis ta zargi Malaman addini da laifin sabawa umurninta wajen dakile yaduwar cutar Korona a fadin tarayya ta yadda suke tara jama'a a wuraren ibada.

Sakataren gwamnatin tarayya kuma shugaban kwamitin yaki da cutar, Boss Mustapha, ya bayyana hakan a hira da manema labarai a birnin tarayya Abuja.

Yace, "Mun lura cewa wasu yan Najeriya, musamman kungiyoyin addini sun cigaba da gudanar da shirye-shiryensu da ka iya kara yaduwan cutar."

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel