Buhari ya sanar da gwamnoni hanyar da za su bi wurin magance rashin tsaro

Buhari ya sanar da gwamnoni hanyar da za su bi wurin magance rashin tsaro

- Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bukaci gwamnoni su yi aiki da shugabannin gargajiya

- A cewarsa, aiki dasu ne kadai zai bai wa gwamnati damar sanin halin da al'umma take ciki, da labarai a kan 'yan ta'adda

- Shugaba Buhari ya fadi hakan ne a wani taro da yayi da gwamnonin jihohi 36, inda suka tattauna a kan halin da kasa take ciki

A taron da shugaba Buhari yayi da gwamnoni, ya zauna tsaf ya saurari korafi daga yankuna 6 da ke kasar nan, daga bakin gwamnoni, a kan harkokin tsaro da ke addabar kasarnan.

Kamar yadda kakakin shugaban kasa, Garba Shehu yace, shugaban kasa ya ce, "Wajibi ne gwamnati tayi aiki tare da shugabannin gargajiya. Ya kamata a hada kai dasu don a san ta inda za a bullo wa lamarin."

Buhari ya ce mulkinsa ya yi kokarin gyara yankunan arewa maso gabas da kudu-kudu, amma yankin kudu-kudu suna cikin mawuyacin hali, Daily Trust ta wallafa.

Buhari ya sanar da gwamnoni hanyar da za su bi wurin magance rashin tsaro
Buhari ya sanar da gwamnoni hanyar da za su bi wurin magance rashin tsaro. Hoto daga @MobilePunch
Asali: Twitter

KU KARANTA: Budurwa ta banka wa saurayinta wuta saboda ya ki aurenta (Hotuna)

"Kullum ina samun labarin wata baraka da kuma fasa bututun man fetur. Ya kamata a dakatar da satar mai," inji Buhari.

Yayin da shugaban kasa yake magana a kan al'amarin ta'addanci da garkuwa da mutane a kowanne yanki, ya ce wajibi ne a tabbatar an kare kasa daga ta'addanci.

"Za mu tabbatar sojoji sun kawo karshen duk wasu 'yan ta'adda da masu garkuwa da mutane."

Ya ce dalilin rufe iyakar kasa duk don a kiyaye shigowa da miyagun makamai da kwayoyi ne.

"Amma yanzu haka muna son mu bude iyakokin kasar nan kusa," a cewarsa.

Shugaba Buhari ya tabbatar wa da 'yan Najeriya cewa za su yi iyakar kokarinsu wurin ganin karshen ta'addanci a kasar nan.

KU KARANTA: Bayan kama budurwarsa tana cin amanarsa, saurayi ya bukaci shawara a kan abinda ya dace da ita

A wani labari na daban, Femi Adesina, mai ba wa shugaban kasa shawara na musamman a kan yada labarai, ya ce Shugaba Muhammadu Buhari ya tabbatar wa gwamnonin jihohi 36 cewa mulkinsa ya zage damtse wurin kawo karshen rashin tsaro a kasar nan.

A wani taro da aka yi a ranar Talata, 8 ga watan Disamba, gwamnan jihar Borno, Babagana Zulum da takwarorinsa na jihohin arewa maso gabas basu tayar da zancen kawo wasu mayaka ba don kawar da 'yan ta'addan Boko Haram a yankinsu.

The Punch ta ruwaito yadda Zulum ya bayyana bukatunsa 6 ga gwamnatin tarayya don kawo karshen ta'addancin 'yan Boko Haram bayan kashe manoman shinkafa 43 da suka yi a Borno, watan da ya gabata.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel