Buhari ya sake nada Ahmed Kuru a matsayin MD na AMCON, Aminu a matsayin Darekta

Buhari ya sake nada Ahmed Kuru a matsayin MD na AMCON, Aminu a matsayin Darekta

- Shugaban kasa, Muhammadu Buhari, ya yi wasu muhimman nade-nade a hukumomin NDIC da AMCON

- Sanar da sabbin nade-nade na kunshe a cikin sanarwar da kakakin shugaban kasa, Garba Shehu, ya fitar ranar Litinin

Shugaban kasa, Muhammadu Buhari, ya sake zaben Ahmed Kuru a matsayin manajan darekta a hukumar kula da kadarori ta kasa (AMCON).

Kazalika, ya amince da nada Eberechukwu Uneze da Aminu Isma'il a matsayin darektoci ma su cikakken iko na zangon wa'adin shekaru biyar.

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da kakakin shugaban kasa, Garba Shehu, ya fitar a ranar Litinin.

DUBA WANNAN: A villa ake iskanci na gaske kuma Buhari ne jagora; Aisha ta mayar da martani a kan gargadin shugaba Buhari

A cewar Garba Shehu, shugaba Buhari ya aika sunayen mutanen zuwa majalisar dattijai domin neman amincewarta.

Buhari ya sake nada Ahmed Kuru a matsayin MD na AMCON, Aminu a matsayin Darekta
Buhari ya sake nada Ahmed Kuru a matsayin MD na AMCON, Aminu a matsayin Darekta @Buhari Sallau
Asali: Facebook

Kazalika, shugaba Buhari, a cikin wata wasikar daban, ya nemi majalisar dattijai ta amince da nadin Mista Bello Hassan a matsayin manajan darekta a hukumar NDIC.

DUBA WANNAN: Kungiyar Malaman Kano ta magantu a kan batun goyawa takarar Tinubu baya a 2023

A cikin wasikar, Buhari ya nemi majalisar ta amince da nadin Mustapha Muhammad Ibrahim a matsayin darektan mai cikakken iko a hukumar.

Legit.ng Hausa ta rawaito cewa gwamnan Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, ya ce duk da kisan da mayakan kungiyar Boko Haram ke yi a Jihar, tsaro ya karu a jihar a karkashin mulkin shugaban kasa, Muhammadu Buhari.

Farfesa Zulum, ya bayyana hakan ne ranar Lahadi yayin da ya karbi bakuncin kungiyar dattijan arewa a karkashin jagorancin shugabanta, Ambasada Shehu Malami, da kuma sakatarenta, Audu Ogbeh.

Hakan na kunshe ne a cikin jawabin da gwamnatin jihar Borno ta fitar ranar Litinin mai taken 'Zulum: Duk da kashe-kashe, shaidu a kasa sun nuna cewa an fi samun zaman lafiya a karkashin mulkin Buhari a Borno.

Don sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel