Buhari ya sake nada Ahmed Kuru a matsayin MD na AMCON, Aminu a matsayin Darekta

Buhari ya sake nada Ahmed Kuru a matsayin MD na AMCON, Aminu a matsayin Darekta

- Shugaban kasa, Muhammadu Buhari, ya yi wasu muhimman nade-nade a hukumomin NDIC da AMCON

- Sanar da sabbin nade-nade na kunshe a cikin sanarwar da kakakin shugaban kasa, Garba Shehu, ya fitar ranar Litinin

Shugaban kasa, Muhammadu Buhari, ya sake zaben Ahmed Kuru a matsayin manajan darekta a hukumar kula da kadarori ta kasa (AMCON).

Kazalika, ya amince da nada Eberechukwu Uneze da Aminu Isma'il a matsayin darektoci ma su cikakken iko na zangon wa'adin shekaru biyar.

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da kakakin shugaban kasa, Garba Shehu, ya fitar a ranar Litinin.

DUBA WANNAN: A villa ake iskanci na gaske kuma Buhari ne jagora; Aisha ta mayar da martani a kan gargadin shugaba Buhari

A cewar Garba Shehu, shugaba Buhari ya aika sunayen mutanen zuwa majalisar dattijai domin neman amincewarta.

Buhari ya sake nada Ahmed Kuru a matsayin MD na AMCON, Aminu a matsayin Darekta
Buhari ya sake nada Ahmed Kuru a matsayin MD na AMCON, Aminu a matsayin Darekta @Buhari Sallau
Asali: Facebook

Kazalika, shugaba Buhari, a cikin wata wasikar daban, ya nemi majalisar dattijai ta amince da nadin Mista Bello Hassan a matsayin manajan darekta a hukumar NDIC.

DUBA WANNAN: Kungiyar Malaman Kano ta magantu a kan batun goyawa takarar Tinubu baya a 2023

A cikin wasikar, Buhari ya nemi majalisar ta amince da nadin Mustapha Muhammad Ibrahim a matsayin darektan mai cikakken iko a hukumar.

Legit.ng Hausa ta rawaito cewa gwamnan Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, ya ce duk da kisan da mayakan kungiyar Boko Haram ke yi a Jihar, tsaro ya karu a jihar a karkashin mulkin shugaban kasa, Muhammadu Buhari.

Farfesa Zulum, ya bayyana hakan ne ranar Lahadi yayin da ya karbi bakuncin kungiyar dattijan arewa a karkashin jagorancin shugabanta, Ambasada Shehu Malami, da kuma sakatarenta, Audu Ogbeh.

Hakan na kunshe ne a cikin jawabin da gwamnatin jihar Borno ta fitar ranar Litinin mai taken 'Zulum: Duk da kashe-kashe, shaidu a kasa sun nuna cewa an fi samun zaman lafiya a karkashin mulkin Buhari a Borno.

Don sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng