Allah ya yi wa tsohon gwamnan Kaduna, Balarabe Musa rasuwa

Allah ya yi wa tsohon gwamnan Kaduna, Balarabe Musa rasuwa

- Tsohon gwmnan Kaduna, Alhaji Abdulkadir Balarabe Musa ya rasu

- Marigayin ya rasu ne a safiyar ranar Laraba a gidansa da ke Aliyu Turaki Road Unguwar Sarki Kaduna

- Ya rasu yana da shekaru 84 a duniya kuma za ayi jana'izarsa a yau Laraba

Rahotannin da muka samu ta tabbatar da rasuwar tsohon gwamnan Jihar Kaduna Abdulkadir Balarabe Musa.

'Yar marigayin ta tabbatar da cewa ya rasu a safiyar ranar Laraba a kamar yadda The Cable ta ruwaito.

A cewarta, za ayi masa jana'iza a yau da rana.

Tsohon sanata mai wakiltar mazabar Kaduna ta tsakiya, Shehu Sani shima ya sanar da rasuwar tsohon gwamnan a shafinsa na Twitter a ranar Laraba 11 ga watan Nuwamba.

KU KARANTA: Wanda ya yi ƙarar Rahama Sadau ya ce fadar shugaban kasa da wani kwamishinan 'yan sanda ke hana a kama ta

Allah ya yi wa tsohon gwamnan Kaduna, Balarabe Musa rasuwa
Allah ya yi wa tsohon gwamnan Kaduna, Balarabe Musa rasuwa. Hoto: @thisdaylive
Asali: Twitter

A sakon da ya wallafa a Twitter, Shehu Sani ya rubuta "Alhaji Balarabe Musa ya rasu a yau. Allah ya jikan rai ya kuma saka masa da gidan Aljanna Firdausi. Amin."

DUBA WANNAN: Rahama Sadau ta yi magana kan rahotannin kama ta da gurfanar da ita a kotu

Balarabe Musa ne gwamna na farko da aka fara tsige wa a tarihin Najeriya.

Har wa yau, shine shugaban jam'iyyar People’s Redemption Party (PRP) a jamhuriyya ta hudu amma ya sauka daga mukamin a shekarar 2018 saboda ya kula da lafiyarsa.

A wani labarin, kungiyar kare hakkin musulmi (MURIC) ta bukaci a kama kuma a gurfanar da Rev. Fr. Godfrey Igwebuike Onah, wata huduba da ya yi a coci na tunzura matasan kiristoci a Nsukka, jihar Enugu, da su kai hari kan musulmai da kuma lalata masallatai a garin.

Shugaban MURIC, Ishaq Akintola, wanda ya yi wannan batun a ranar Juma'a a wata sanarwa, ya ce kungiyar ta goyi bayan Majalisar Ƙolin Harkokin Addinin Musulunci (NSCIA) a karar da ta shigarwa DSS na a kama tare da gurfanar da Rev. Onah.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164