Da duminsa: Jigo a fadar Buhari ya rasu sakamakon ciwon kansa

Da duminsa: Jigo a fadar Buhari ya rasu sakamakon ciwon kansa

- Fadar shugaban kasa ta fada alhini da makokin rasuwar Babatunde Lawal sakamakon ciwon kansa

- Lawal mai shekaru 56 ya rasu a ranar Juma'a, 6 ga watan Nuwamba, bayan shekaru biyu da nada shi babban sakatare

- A sakon ta'aziyyar sakataren gwamnatin tarayya, Boss Mustapha ya kwatanta mutuwar Lawal da ikon Allah

Babatunde Lawal, babban sakataren a ofishin sakataren gwamnatin tarayya, Boss Mustapha, ya rasu.

Lawal ya rasu a ranar Juma'a, 6 ga watan Nuwamba bayan fama da cutar kansar hanta da yayi. Ya rasu bayan daukar shekaru biyu da yayi a kan mukaminsa.

Masani ne a fannin tattalin arziki tare da tsari. Ya fara aiki da gwamnatin tarayya a watan Oktoban 1987 a matsayin jami'in tsari a ma'aikatar tsari da tattali ta tarayya.

Mamacin ya yi aiki a wurare da dama wadanda suka hada da mamba a kwamitin asusun tarayya da kuma kudin shiga kuma yayi aiki da NBS.

A daya bangaren, SGF Mustapha ya nuna damuwarsa tare da alhininsa a kan mutuwar Lawal, ya kwatanta rasuwarsa da ikon Allah.

A wata takarda da babban sakataren ofishin SGF ya fitar, Maurice Nnamdi Mbaeri, Mustapha ya ce ya matukar damuwa da mutuwar Lawal.

KU KARANTA: Da gangan na dinga lalata da kanwar matata don in bata mata rai - Magidanci

Da duminsa: Jigo a fadar Buhari ya rasu sakamakon ciwon kansa
Da duminsa: Jigo a fadar Buhari ya rasu sakamakon ciwon kansa. Hoto daga Thisday.com
Asali: UGC

KU KARANTA: Buhari: Ba zai yuwu mu cigaba da tsame matasa ba wurin yanke hukunci

A wani labari na daban, Gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya musanta sanin masu hada hotunansa a fosta da sunan kamfen dinsa a matsayin mataimakin shugaban kasa a zaben 2023 dake gabatowa.

Gwamnan ya sanar da hakan ne yayin da yake amsa tambayoyin manema labarai bayan haduwarsa da mataimakin shugaban kasa, Farfesa Yemi Osinbajo a fadar shugaban kasa da ke Abuja, ranar Juma'a.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Khalid avatar

Aisha Khalid (Hausa editor) Aisha Khalid marubuciyar jaridar Legit.ng ce mai fatan shahara. Ta samu digirinta na farko a jami'ar Ahmadu Bello da ke Zaria a shekarar 2018. Ta kwashe shekaru tana rubutu a fannonin siyasa, nishadi, tsegumi da sauransu. Za a iya tuntubar ta a adireshin email din ta kamar haka: aisha.khaleed@corp.legit.ng