An sako ɗan uwan tsohon Sarkin Kano Sanusi da aka yi garkuwa da shi

An sako ɗan uwan tsohon Sarkin Kano Sanusi da aka yi garkuwa da shi

- Masu garkuwa da mutane sun sako Aminu Musa Abdaullahi dan uwan tsohon sarki Muhammadu Sanusi II

- Hakan na zuwa ne bayan ya yi kwanaki hudu a hannun masu garkuwar da suka sace shi a hanyar Abuja zuwa Kaduna

- An sako shi a daren ranar Lahadi kamar yadda wata majiya daga iyalan gidan ta sanar kuma ba a san ko an biya kudin fansa ba

An sako Aminu Musa Abdullahi dan uwan tsohon sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II daga hannun masu garkuwa.

An sace shi ne a hanyar babban birnin tarayya Abuja zuwa Kaduna a makon da ta gabata kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.

An sako dan uwan tsohon Sarkin Kano Sanusi da aka yi garkuwa da shi
Sarki Muhammadu Buhari. Hoto: @daily_trust
Asali: Twitter

DUBA WANNAN: Manyan 'yan siyasa sun hallarci ɗaurin auren ɗan Aliero da 'yar Yariman Bakura a Sokoto

Wata majiya na kusa da iyalan tsohon sarkin ta ce Abdullahi da aka fi sani da Yaya Baba ya dawo gida bayan shafe kwanaki hudu a hannun masu garkuwa.

Ya dawo cikin koshin lafiya a daren ranar Lahadi kamar yadda majiyar ta bayyana.

A halin yanzu ba a tabbatar ko an biya kudin fansa kafin a sako shi ba ko kuma ba a biya ba.

KU KARANTA: Wani dan shekara 69 ya yi ikirarin ya saki matarsa don ta zabi Joe Biden a zaben Amurka

A wani labarin, kungiyar kare hakkin musulmi (MURIC) ta bukaci a kama kuma a gurfanar da Rev. Fr. Godfrey Igwebuike Onah, wata huduba da ya yi a coci na tunzura matasan kiristoci a Nsukka, jihar Enugu, da su kai hari kan musulmai da kuma lalata masallatai a garin.

Shugaban MURIC, Ishaq Akintola, wanda ya yi wannan batun a ranar Juma'a a wata sanarwa, ya ce kungiyar ta goyi bayan Majalisar Ƙolin Harkokin Addinin Musulunci (NSCIA) a karar da ta shigarwa DSS na a kama tare da gurfanar da Rev. Onah.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164