COVID-19: Za a gudanar da bincike a kan bacewar N6.2b a NDDC - Majalisa

COVID-19: Za a gudanar da bincike a kan bacewar N6.2b a NDDC - Majalisa

- ‘Yan Majalisar Tarayya su na binciken zargin awon gaba da kudi a NDDC

- Majalisar Wakilai ta na kuma bibiyar facaka da aka yi a NBET da NIMET

- Babban mai binciken kudin kasa ya na zargin cewa an wawuri wasu kudi

Majalisar wakilan tarayya a Najeriya ta kai ga fara binciken zargin badakala a ma’aikatar NDDC mai kula da cigaban yankin Neja-Delta.

Jaridar Punch ta ce ‘yan majalisar su na binciken wasu makudan kudi har Naira biliyan 6.2 da ake zargin an yi awon gaba da su a NDDC.

Ana zargin an karkatar da wadannan kudi da aka ware domin bada tallafin COVID-19 a yankin.

KU KARANTA: Masu tada hatsaniya da sunan #EndSARS za su yaba wa aya zaki a Nasarawa

Bayan nan kuma majalisar wakilai ta na kuma binciken barnar Naira biliyan 139.317 da ofishin mai binciken kudi na kasa ya ke ikirari.

Rahoton ya bayyana cewa OAGF ya na zargin an tafka wannan barna ne tsakanin 2013 da 2018.

Sai dai an gamu da cikas wajen binciken, dole ‘yan majalisar su ka dakata da aikinsu a dalilin rashin halartar shugabannin ma’aikatar NDCC.

Sauran wadanda su ka gagara hallara a majalisa wajen wannan bincike sun hada da shugabannin ma’aikatar saida wuta da NIMET.

KU KARANTA: Fatima Ganduje ta na nadamar abu 1 da ta yi a Najeriya

COVID-19: Za a gudanar da bincike a kan bacewar N6.2b a NDDC - Majalisa
Kakakin Majalisa Hoto: vanguardngr.com
Asali: UGC

‘Yan majalisar su na kuma bibiyar abin da ma’aikatar Neja-Delta ta yi da kudinta tsakanin Junairun 2018 zuwa ranar 30 ga watan Yuni, 2018.

Hakan ya biyo bayan binciken kudin da gwamnatin tarayya ta yi wanda ta tike a Disamban 2018. An saurari ta bakin jama’a a wajen binciken.

A makon nan ne ku ka ji cewa shugaban kasa Muhammadu Buhari ya nada Sanata Oladipo Olusoga Odujinrin a matsayin shugaban NACA.

Olusoga Odujinrin zai rike mukamin shugaban wucin gadi na masu bada shawara a hukumar.

Idan ku na da wata shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Asali: Legit.ng

Authors:
Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng