Obasanjo: Hallaka masu zanga-zangar #EndSARS zai sa a gaza zaman sulhu

Obasanjo: Hallaka masu zanga-zangar #EndSARS zai sa a gaza zaman sulhu

- Olusegun Obasanjo ya soki amfani da karfin bindiga wajen maganin zanga-zanga

- Tsohon shugaban ya ce wannan danyen aiki zai kara hura wutan halin da ake ciki

- Obasanjo ya yi kira ga gwamnatin kasar ta yi maza ta dauki mataki kafin a makara

Tsohon shugaban kasar Najeriya, Olusegun Obasanjo ya yi tir da amfani da karfi da sojoji su ka yi wajen tasa keyar masu zanga-zanga a Legas.

Cif Olusegun Obasanjo ya ce gwamnatin shugaba Muhammadu Buhari ba ta dauki duk sauran matakan da ya kamata kafin ta kai ga baza sojoji ba.

Jaridar Punch ta ce Obasanjo ya yi wannan bayani ne a wani jawabi da ya fitar a game da murkushe masu zanga-zanga da jami’an tsaro ke yi.

KU KARANTA: Gwamnan Legas ya ziyarci 'yan zanga-zanga da aka harbe

Obasanjo ya yi wa jawabin take da: “Statement on Violence Against Protesters In Nigeria: An Appeal for Calm’, ya na kiran a kawo zaman lafiya.

Tsohon shugaban ya gargadi Buhari “a kan amfani da karfin soji da sauran jami’an tsaro wajen yi wa mutane karfa-karfa da nufin shawo kan rikicin.”

Obasanjo wanda ya mulki Najeriya tsakanin 1999 da 2007 ya ce tarihi ya nuna kashe masu zanga-zanga bai kawo kwanciyar hankali, sai ma akasinsa.

Tsohon Janar din ya ce amfani da kan bindiga zai sa a gaza iya zama a kan tebur domin ayi sulhu.

KU KARANTA: Gwamnonin Arewa sun yi gargadi a kan shirya zanga-zanga

Obasanjo: Hallaka masu zanga-zangar #EndSARS zai sa a gaza zaman sulhu
Obasanjo Hoto: www.blueprint.ng
Asali: UGC

A jawabinsa, Obasanjo ya yi kira ga shugaban kasan ya yi maza ya dauki mataki tun kafin abubuwa su yi kamari, a rasa yadda za ayi a fadin kasar.

“An yi ta’adi, amma za a iya shawo kan lamarin kafin ya rincabe gaba daya.” Inji Obasanjo.

Dazu Dahiru Bauchi ya ja-kunnen gwamnati, ya fada mata cewa ba a kashe wuta da wuta, don haka shugaba Buhari ya nemi ya sasanta da masu zanga-zanga.

Shehin malamin ya ce idan aka yi sake karshen zangar-zangar #EndSARS ba zai yi kyau ba.

Idan ku na da wata shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Asali: Legit.ng

Online view pixel