Da ɗuminsa: Gwamnatin Edo ta sanya dokar ta ɓaci ta awanni 24 a fadin jihar

Da ɗuminsa: Gwamnatin Edo ta sanya dokar ta ɓaci ta awanni 24 a fadin jihar

- Gwamnan jihar Edo, Godwin Obaseki ya saka dokar hana fita na sa’o’i 24

- Wannan mataki ya biyo bayan harin da wasu yan iska suka aiwatar a safiyar yau Litinin

- Gwamnatin ta Edo ta kuma bayyana cewa dokar za ta fara aiki daga karfe 4:00 na rana

Gwamnatin jihar Edo ta sanar da sanya dokar hana fita na sa’o’i 24 a fadin jihar.

Dokar za ta fara aiki daga karfe 4:00pm na ranar 19 ga watan Oktoba, har sai baba-ta-gani.

Babban sakataren gwamnatin jihar, Osarodion Ogie ne ya fitar da sanarwar, Channels TV ta ruwaito.

Ogie ya bayyana cewa an sanya takunkumin ne sakamakon hare-haren da wasu yan iska da suka mamaye zanga-zangar #ENDSARS suka aiwatar.

KU KARANTA KUMA: Sauya salon zanga-zanga: An sako sojoji zuwa titunan Abuja

Akwai bukatar daukar wannan mataki saboda lamarin barna da hare-hare da yan iska wadanda suka fake da zanga-zangar #ENDSARS suka kai kan mutane.

“Yayinda gwamnatin jihar Edo ke mutunta yancin al’ummanta na gudanar da zanga-zangar lumana, ba za ta zauna ta zuba ido tana kallon yan iska su dauki doka a hannunsu ba domin haifar da rikici a kan al’umman da basu ji ba basu gani ba da jihar,” in ji Ogie.

An bukaci makarantu da wuraren kasuwanci su rufe harkokinsu bayan sanarwar.

KU KARANTA KUMA: Ruth Inomina: Mutumiyar Neja-Delta ta samu shiga Sojan ruwan USMV

Da ɗuminsa: Gwamnatin Edo ta sanya dokar ta ɓaci ta awanni 24 a fadin jihar
Da ɗuminsa: Gwamnatin Edo ta sanya dokar ta ɓaci ta awanni 24 a fadin jihar Hoto: @MobilePunch
Asali: Twitter

An shawarci mutane da su dakatar da zirga-zirga daga yanzu zuwa 4:00pm har sai an dawo da zaman lafiya.

Wasu yan iska a safiyar ranar Litinin sun mamaye sanya-zangar kawo karshen rundunar SARS a birnin Benin.

Babban mai bayar da shawara ga Godwin Obaseki a kafofin watsa labarai, Crusoe Osagie, ya fada ma Channels TV cewa yan iskan sun yi musayar wuta da jami’an tsaro a wani kurkuku da ke birnin Benin.

A yanzu haka, yan iskan na musayar wuta da jami’an tsaro a Oko, birnin Benin,” in ji.

A baya mun ji cewa dumbin mazauna wani gidan yari da ke birnin Benin a jihar Edo sun samu damar tserewa bayan wasu batagari da ake kyautata zaton 'yan daba ne sun balle gidan yarin.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng