Sauya salon zanga-zanga: An sako sojoji zuwa titunan Abuja

Sauya salon zanga-zanga: An sako sojoji zuwa titunan Abuja

- Zanga-zangar neman a rushe rundunar SARS ta fara sauya salo a sassan Najeriya da ta samu karbuwa

- Rahotannin baya bayan nan sun nuna cewa ana yawan samun kai hari a kan ma su zanga-zangar adawa da ma su zanga-zangar nuna goyon bayan rundunar SARS

- Rundunar sojin Najeriya ta sanar da cewa atisayen 'murmushin kada' da ta kaddamar bashi da alaka da kowacce zanga-zanga

An fito da dakarun soji zuwa kan titunan Abuja domin shawo kan zanga-zangar ENDSARS da ta fara sauya salo.

Zanga-zangar ENDSARS a Abuja ta fara sauya salo tare da neman rikidewa zuwa rikici sakamakon harin da wasu batagari ke kaiwa ma su zanga-zangar.

Batagari a Abuja na kai hari kan ma su zanga-zangar nuna adawa da rundunar SARS da kuma ma su zanga-zangar nuna goyon bayan rundunar SARS.

Lamarin, a yawancin lokuta, ya haddasa gumurzu tare da zama sanadiyyar raunata mutane da kuma lalata dukiya.

KARANTA: Duk don a rusa gwamnatin Buhari ne - Sheikh Jingir ya fadi manufar masu zanga-zanga

Wasu rahotanni sun bayyana cewa wani daga cikin ma su zanga-zanga ya rasa ransa a asibitin da aka kai shi sakamakon mummunan rauni da wasu batagari suka yi masa a Abuja.

An ga dakarun soji da safiyar ranar Litinin a sanannen shataletalen AYA, wurin da masu zanga-zanga su ka yi niyyar mamayewa.

Sauya salon zanga-zanga: An sako sojoji zuwa titunan Abuja
Sauya salon zanga-zanga: An sako sojoji zuwa titunan Abuja
Asali: UGC

Jaridar The Nation ta rawaito cewa an ga dakarun soji sun saka garkuwa a kan titin domin tabbatar da cewa ma su zanga-zangar basu rufe hanya tare da haddasa cunkuso ba.

KARANTA: Yadda na samo mana kwangilar tono kabari a kan N2m - Abdullahi Dogo

A jiya, Lahadi, ne rundunar soji ta sanar da cewa sabon atisayen 'murmushin kada' da ta kaddamar bashi da wata nasaba da zanga-zangar da matasa ke yi a kan rushe rundunar SARS da zaluncin 'yan sanda.

A cikin wata sanarwa da hedikwatar tsaro ta fitar (DHQ), kanal Sagir Musa, kakakin rundunar soji ya ce kuskure ne a bayyana cewa an kaddamar da atisayen ne saboda zanga-zangar ENDSARS da ake yi a sassan kasa.

Kanal Sagir ya bayyana cewa rundunar soji ta nuna kwarewar aiki tun bayan barkewar zanga-zangar kusan sati biyu da su ka wuce.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng