Tunda gwamnati ta amsa kokenku lokaci ya yi da ya kamata a daina wannan zanga-zanga - Lawan ga matasa

Tunda gwamnati ta amsa kokenku lokaci ya yi da ya kamata a daina wannan zanga-zanga - Lawan ga matasa

- Shugabannin majalisar dokokin tarayya sun bukaci a kawo karshen zanga-zangar rushe rundunar SARS

- Lawan Ahmed ya ce tunda dai gwamnati ta amsa bukatun masu zanga-zangar kamata yayi yanzu su koma gida

- Ya ce lamarin na matukar takura wa jama'a da ke kasuwancinsu

Shugaban majalisar dattijai na kasar, Ahmed Lawan, ya yi kira ga masu zanga-zangar neman kawo karshen rundunar SARS a fadin Najeriya da su yi hakuri su dakatar da zanga-zangar.

Lawan ya bayyana hakan ne bayan ganawar da ya gudana tsakaninsa da Shugaban kasa, Muhammadu Buhari da kuma kakakin majalisar wakilai, Femi Gbajabiamila.

Sun yi ganawar ne a yau Lahadi, 18 ga watan Oktoba, a fadar shugaban kasa da ke Abuja.

Lawan ya jadadda cewa ya kamata masu zanga-zangar su janye tunda sun gabatar da kokunsu kuma gwamnati ta dauki mamaki kan haka.

Ya kara da cewa wannan zanga-zanga da ake yi yana takura wa al’umma musamman masu gudanar da harkokin kasuwancinsu.

Tunda gwamnati ta amsa kokenku lokaci ya yi da ya kamata a daina wannan zanga-zanga - Lawan ga matasa
Tunda gwamnati ta amsa kokenku lokaci ya yi da ya kamata a daina wannan zanga-zanga - Lawan ga matasa Hoto: @THISDAYLIVE
Asali: Facebook

Ya kuma ce hakan na kawo cikas ga tattalin arzikin kasar.

KU KARANTA KUMA: Tsaron Arewa: Ali Nuhu ya sha caccaka a wajen 'yan Najeriya saboda rashin shiga zanga-zanga

“Tun da gwamnati ta amince da bukatun da masu zanga-zangar suka gabatar mata, lokaci ya yi da masu zanga-zangar za su daina, gwamnati na bukatar lokaci domin aiwatar da bukatun masu zanga-zangar,” in ji Lawan.

A nashi bangaren, kakakin majalisar wakilai, Gbajabiamila ya yi kira ga kawo karshen zanga-zangar, inda ya bayyana cewa ba za a iya aiwatar da manufa a dare daya ba.

Ya kuma jinjinawa masu sanya-zangar a kan namijin kokarin da suka yi, ya basu tabbacin cewa suna iya ci gaba da zanga-zangar idan ba a cika masu bukatunsu ba a makonni biyu.

A baya mun kawo cewa Shugaban kasa Muhammadu Buhari da shugabannin majalisar dokokin tarayya na cikin wata ganawar sirri a yanzu haka.

Hadimin Shugaban kasa Buhari na musamman a shafukan zumuntar zamani, Bashir Ahmad ne ya tabbatar da hakan a wata wallafa da ya yi a shafinsa na Twitter, @BashirAhmaad a ranar Lahadi, 18 ga watan Oktoba.

KU KARANTA KUMA: Bidiyon wani mai bayar da hannu a titi da masu zanga-zanga suka karrama saboda kwazonsa

A cewar Ahmad, Shugaban kasar na ganawa da Shugaban majalisar dattawa Ahmad Lawan da kakakin majalisar wakilai, Femi Gbajabiamila kan zanga-zangar da ke gudana.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng