An aika takardar korafi a kan Buhari zuwa UK da USA saboda nadin wani mukami

An aika takardar korafi a kan Buhari zuwa UK da USA saboda nadin wani mukami

- Har yanzu batun aika sunan hadimar Buhari, Lauretta Onochie, a matsayin kwamishina a hukumar zabe ya na cigaba da jawo cece-kuce

- Jam'iyyar PDP da dumbin sauran 'yan Najeriya sun nuna adawa da yunkurin Buhari na son bawa Lauretta wannan muhimmin mukami

- Yanzu haka har wata kungiya mai rajin kare mutuncin Najeriya ta aika takardar korafi a kan Buhari zuwa Ingila da Amurka

Wata kungiya mai rajin kare mutuncin Najeriya (Concerned Nigerians) ta yi Allah wadai da yunkurin shugaba Buhari na son nada Lauretta Onochie a matsayin kwamishiniya a hukumar zabe ta kasa (INEC).

Kungiyar ta roki Amurka, Ingila, da sauran ma su fada a ji a duniya a kan su kawowa Najeriya agaji saboda Buhari ya na shirin lalata siyasar kasa da kassara hukumar INEC.

A takardar da kungiyar ta rubuta ranar Alhamis, 14 ga watan Oktoba, ta sanar da USA da UK cewa nadin Lauretta ya sabawa kundin tsarin mulkin Najeriya.

DUBA WANNAN: Muhimman aiyuka 8 na sabuwar rundunar SWAT - NPF

"Kowa ya san 'yar siyasa ce da ke dauke da katin shaidar zama mamba a jam'iyyar APC mai mulki.

An aika takardar korafi a kan Buhari zuwa UK da USA saboda nadin wani mukami
Lauretta Onochie
Asali: UGC

"Ba iya wannan ne kadai matsalar ba, ta yi kaurin suna wajen ragargaza da cin mutuncin duk wanda ya soki jam'iyyar APC.

"Nada Lauretta, hadimar shugaban kasa, a matsayin kwamishiniya a INEC mai wakiltar jihar Delta ya sabawa kundin tsarin mulki kuma yunkuri ne na lalata kima da martabar hukumar zabe," a cewar takardar mai dauke da sa hannun shugaban kungiyar, Deji Adeyanju.

KARANTA WANNAN: Neymar ya aika wa Cristiano Ronaldo wasika bayan kamuwa da cutar COVID-19

Har yanzu yumkurin shugaba Buhari na son nada Lauretta na cigaba da yamutsa hazo a cikin kasa.

Babbar jam'iyyar adawa, PDP, da sauran dumbin 'yan Najeriya sun nuna rashin amincewa da niyyar shugaba Buhari ta nada Lauretta a mukami mai muhimmanci kamar kwamishiniya a hukumar INEC.

A wani labarin, hukumar da ke kula da matasa masu yiwa kasa hidima NYSC a jihar Anambra ta hada liyafar taya matasa 12 murnar yin aure a yayin bautar kasarsu ta shekara daya a jihar.

Ma'auratan da suka hadu a rukunin C na masu yiwa kasa hidimar na shekarar 2019, sun hada da Henry Nwachoko, Charles Ruth, Oluchukwu Davis, da Ohale Nkemakolam.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng