Bayan nada shi sarkin Zazzau, Ahmed Bamalli ya shiga fada

Bayan nada shi sarkin Zazzau, Ahmed Bamalli ya shiga fada

- Alhaji Ahmed Bamalli, sabon sarkin Zazzau, ya shiga fadar masarautar

- Sakataren gwamnatin jihar Kaduna, Balarabe Abbas Lawal, na tare da Bamalli a lokacin da ya isa Fadar Sarkin Zazzau

- A yau Laraba, 7 ga watan Oktoba ne Gwamna Nasir El-Rufai ya sanar da nada Bamalli a matsayin sarkin Fulanin Zazzau na 19

Bayan nada shi a matsayin sabon sarkin Zazzau, Alhaji Ahmed Bamalli, ya shiga fadar masarautar a yau Laraba, 7 ga watan Oktoba, jaridar Aminiya ta ruwaito.

An tattaro cewa sakataren gwamnatin jihar Kaduna, Balarabe Abbas Lawal, na tare da Bamalli a lokacin da ya isa Fadar Sarkin Zazzau.

Hotunan bidiyo da aka wallafa a shafukan sada zumunta sun nuna tawagar sabon sarkin na Zazzau tana isa fadarsa da ke birnin Zaria.

A cikin bidiyon isowar sarkin Fada, an ga mutane da dama suna yi masa rakiya tare da yi masa kirari da san barka.

Ga bidiyon isowar sabon sarkin a kasa:

KU KARANTA KUMA: Allahu Akbar: Sakataren masarautar Kano, Muhammadu Bayero ya rasu

Bayan nada shi sarkin Zazzau, Ahmed Bamalli ya shiga fada
Bayan nada shi sarkin Zazzau, Ahmed Bamalli ya shiga fada Hoto: @aminiyatrust
Asali: Twitter

Bamalli, wanda kafin nadinsa shi ne Magajin Garin Zazzau a yanzu baya cikin ‘yan takara uku da Masu Zabar Sarki na masarautar suka tura wa Gwamna Nasiru El-Rufai da farko.

Ana ganin kusancinsa da gwamnan ta taka rawa wajen neman a sake lalen sunaye ukun amma Masu Zabar Sarkin suka ce sun yi zaben ne bisa adalci.

KU KARANTA KUMA: Sulaiman Dabo ya ce Gwamnan Kaduna bai kawo kudirin raba Masarauta ba

A yau Laraba ne muka samu sanarwar gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir Ahmad El-Rufai na sabon Sarkin Zazzau.

Kamar yadda Gwamnan jihar Kaduna ya wallafa a shafinsa na Twitter, ya bayyana Ahmed Nuhu Bamalli a matsayin Sarkin Zazzau na 19.

Ya gaji marigayi mai martaba, Alhaji Dakta Shehu Idris wanda ya rasu a ranar Lahadi, 20 ga watan Satumban 2020 bayan kwashe shekaru 45 da yayi a karagar mulkin.

Kamar yadda takardar ta bayyana, "Gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir Ahmed El-Rufai, ya amince da nadin Alhaji Ahmed Nuhu Bamalli a matsayin sarkin Zazzau na 19.

"Ya maye gurbin marigayi Alhaji Dakta Shehu Idris, wanda ya rasu a ranar Lahadi, 20 ga watan Satumban 2020 bayan kwashe shekaru 45 da yayi a kan karagar mulki. "

Alhaji Ahmed Bamalli shine Sarki na farko daga gidan Mallawa a cikin shekaru 100 tun bayan rasuwar kakansa, Sarki Dan Sidi a 1920."

Idan ku na da wata shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng