Allahu Akbar: Baturen ilimi na birnin tarayya Abuja, Marafa ya rasu

Allahu Akbar: Baturen ilimi na birnin tarayya Abuja, Marafa ya rasu

- Allah ya yiwa mukaddashin sakataren ilimi na birnin tarayya Abuja, Alhaji Umaru Marafa rasuwa

- Ministan babbar birnin tarayya, Malam Malam Muhammad Bello, ya nuna alhini a kan wannan rashi da aka yi

- Marigayin ya amsa kiran mahaliccinsa bayan dan jinya da yayi

Ministan babbar birnin tarayya, Malam Muhammad Bello, ya nuna bakin ciki a kan mutuwar mukaddashin sakataren ilimi, Alhaji Umaru Marafa, wanda ya rasu.

Marigayin ya rasu ne a yammacin ranar Litinin, 28 ga watan Satumba, bayan ya yi fama da yar gajeruwar rashin lafiya.

Bello ya bayyana marigayin a matsayin jajirtacce kuma jami’i mai kwazon aiki wanda ya bayar da gudunmawa sosai a hukumar birnin tarayya.

Allahu Akbar: Baturen ilimi na birnin tarayya Abuja, Marafa ya rasu
Allahu Akbar: Baturen ilimi na birnin tarayya Abuja, Marafa ya rasu Hoto: Ogeneafrican
Source: UGC

Ya yi sharhi a kan tarin aiki da marigayin da tawagarsa a sakatariyar ilimi suke yi domin tabbatar da sake bude makarntun birnin tarayya cikin nasara a yayinda ake farfadowa daga annobar COVID-19, aridar Punch ta ruwaito.

KU KARANTA KUMA: Yadda mayaƙan Boko Haram suka yi amfani da jaki wajen kai wa Gwamna Zulum hari

A wata sanarwa daga babban sakataren labaran ministan birnin tarayya, Anthony Ogunleye, ya ce: “Ministan birnin tarayyan na kuma mika ta’aziyya ga gwamnati da mutanen jihar Neja da masarautar Kontagora, wanda marigayi Umaru Marafa ya kasance yarima a cikinta.

“Ya yi addu’an jin kai ga mamacin sannan ya roki Allah ya ba iyalansa dangana na wannan babban rashi da suka yi.”

KU KARANTA KUMA: Da duminsa: Buhari ya yi manyan nade nade, ya aika wa majalisa da sunaye

A wani labarin kuma, mun ji cewa Allah ya yiwa tsohon babban alkalin jihar Kano, Justis Shehu Atiku rasuwa, jaridar Daily Trust ta ruwaito.

Shehu Atiku ya rasu ne a ranar Lahadi, 27 ga watan Satumba, bayan ya yi fama da yar gajeruwar rashin lafiya.

Kakakin bangaren shari’a na jihar Kano, Baba Jibo Ibrahim ne ya tabbatar da hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng