Sakamakon zaben Ƙananan hukumomi 16: Obaseki ya zarce Ize-Iyamu da ƙuri'u 87,677

Sakamakon zaben Ƙananan hukumomi 16: Obaseki ya zarce Ize-Iyamu da ƙuri'u 87,677

- Hukumar zabe ta saki sakamakon zaben kananan hukumomi 16 a jihar Edo

- Dan takarar jam’iyyar PDP, Godwin Obaseki ne kan gaba zuwa yanzu

- Akwai takarar kuri’u 87,677 tsakaninsa da dan takarar APC, Osagie Ize-Iyamu

Hukumar zabe mai zaman kanta (INEC) na ci gaba da sakin sakamakon zaben gwamnan jihar Edo wanda aka gudanar a ranar Asabar, 19 ga watan Satumba.

Zuwa yanzu dai dan takarar jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP), Godwin Obaseki ne kan gaba. Akwai tazarar kuri’u kimanin guda 87,677 tsakaninsa da dan takarar jam'iyyar All Progressives Congress (APC), Osagie Ize-Iyamu, wanda shine ke biye da shi.

Sahara Reporters ta ruwaito cewa bayan sanar da sakamakon kananan hukumomi 16, Obaseki ne a kan gaba. Saura kananan hukumomi biyu a nan gaba.

Sakamakon zaben Ƙananan hukumomi 16: Obaseki ya zarce Ize-Iyamu da ƙuri'u 87,677
Sakamakon zaben Ƙananan hukumomi 16: Obaseki ya zarce Ize-Iyamu da ƙuri'u 87,677
Asali: Original

KU KARANTA KUMA: Jan hankali: Muhimman abubuwa 5 da suka faru a ranar da aka gudanar da zaben Edo

Ga jerin wadanda aka sanar zuwa yanzu:

1. Karamar hukumar Igueben

APC: 5,189

PDP: 7,870

2. Karamar hukumar Esan ta Arewa maso gabas

APC 6559

PDP 13,579

3. Karamar hukumar Esan ta tsakiya

PDP: 10,694

APC: 6,719

4. Karamar hukumar Ikpoba Okha

PDP: 41, 030

APC: 18, 218

5. Karamar hukuma Owan ta gabas

APC: 19,295

PDP: 14,7626.

6. Karamar hukumar Estaka West

APC: 26,140

PDP: 17,959

7. Karamar hukumar Egor

APC: 10, 202

PDP: 27, 621

8. Karamar hukumar Esan ta yamma

APC - 7,189

PDP - 17,433

9. Karamar hukumar Uhunmwonde

PDP: 10,022

APC: 5,972

10. Karamar hukumar Ovia ta Arewa

APC - 9907

PDP - 16, 987

11. Karamar hukumar Esan south East

APC: 9,237

PDP: 10,563

12. Karamar hukumarsa Oredo

APC: 18,365

PDP: 43,498

13. Karamar hukumar Owan West

APC - 11,193

PDP - 11,485

14. Karamar hukumar Etsako Central

APC - 8359

PDP - 7478

15. Karamar hukumar Akoko Edo

APC - 22,963

PDP - 20,101

16. Karamar hukumar Etsako East

APC - 17, 011

PDP - 10,668

KU KARANTA KUMA: Sakamakon zaben gwamnan jihar Edo: APC na shan kaye

A halin da ake ciki, jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) ta zargi jam’iyyar All Progressives Congress (APC) da matsa wa hukumar zabe mai zaman kanta canja sakamakon zaben gwamna a sassa daban-daban na jihar Edo.

A cikin wata sanarwa a ranar Asabar, Kola Ologbondiyan, babban sakataren jam’iyyar na kasa, ya bukaci Mahmood Yakubu, Shugaban INEC, da kada ya amsa kiran domin hadin kai da zaman lafiyan kasar.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel