Shugaban kasar Ghana Nana Akufo-Addo zai jagoranci kungiyar ECOWAS

Shugaban kasar Ghana Nana Akufo-Addo zai jagoranci kungiyar ECOWAS

Gwamnatin kasar Ghana ta bada sanarwar cewa an zabi shugaba Nana Akufo-Addo a matsayin shugaban kungiyar ECOWAS.

Mai girma Mista Nana Akufo-Addo zai jagoranci wannan kungiya ta kasashen yammacin Nahiyar Afrika na tsawon wa’adi guda.

An zabi Nana Akufo-Addo mai shekara 76 a matsayin sabon shugaban ECOWAS ne a taron da ake yi a Niamey, Jamhuriyar Nijar.

Yanzu haka mafi yawan shugabannin Afrika ta yamma su na kasar Nijar inda ake gudanar da taron kungiyar ECOWAS na 57.

KU KARANTA: Najeriya ta na cikin kasar da ta fi kowace arahar kudin fetur

Jaridar Premium Times ta ce ana wannan zama ne a babban dakin taro na Mahatma Gandhi da ke kasar Nijar.

Shugabannin yankins su na tattaunawa a kan wani zama da majalisar tsaro ta kungiyar ECOWAS ta yi kafin wannan taro mai-ci.

Bayan an zabi sabon wanda zai jagoranci ECOWAS, Nana Akufo-Addo ya tabbatar da wannan nauyi da aka daura masa a jiya.

An zabi Akufo-Addo ne ba tare da hamayya ba domin shi kadai ne wanda ya tsaya takarar neman wannan kujera.

KU KARANTA: COVID-19 za ta iya jawo cututtuka masu hadari su kama Yaran Afika

Shugaban kasar Ghana Nana Akufo-Addo zai jagoranci kungiyar ECOWAS
Nana Akufo-Addo zai rike kungiyar ECOWAS zuwa 2021 Hoto: TV AfricaNET
Asali: Facebook

Nana Akufo-Addo ya rubuta: “A ranar Litinin, 7 ga watan Satumba, 2020, shugabannin kasashe da kungiyar ECOWAS su ka dauki matakin zabena ba tare da hamayya ba a matsayin shugaban ECOWAS na tsawon wa’adi guda na shekara daya.”

A jawabin da sabon shugaban na ECOWAS ya yi a shafinsa na Twitter, ya ce hadin-kan Afrika zai jawowa kowace kasa cigaba.

“Ina kira ga sauran takwarorina su bada gudumuwarsu wajen matakan da za mu dauka, tare da kawowa yankunanmu cigaba.”

Ya ce: “Mutanenmu babu abin da su ke bukata da ya gaza wannan. Da haka za a cinma manufofin ECOWAS na zaman lafiya, cigaba da nasara.”

A baya kun ji cewa sauran abubuwan da shugabannin za su tattauna a kai sun hada da rikicin siyasar kasar Mali da COVID-19.

Idan ku na da wata shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Asali: Legit.ng

Online view pixel