Ya zama dole a dakatar da wannan haukan – Sultan ya yi magana kan kashe-kashen kudancin Kaduna

Ya zama dole a dakatar da wannan haukan – Sultan ya yi magana kan kashe-kashen kudancin Kaduna

Sa’ad Abubakar III, Sultan na Sokoto, ya yi kira ga kawo karshen kashe-kashe a kudancin Kaduna.

Yankin ta fuskanci yawan hare-hare da ya yi sanadiyar rasa rayuka da dukiyoyi.

Da yake magana a taron kungiyar sarakunan arewa a Kaduna a ranar Litinin, 7 ga watan Satumba, basaraken ya bayyana rikicin a matsayin “hauka da ya zama dole a dakatar dashi cikin gaggawa”.

Ya yi kira ga wadanda ke da hannu a kashe-kashen da su daina mummunan aika-aikan, inda ya ce “hakan ya ishe su.”

Sultan ya ce: “babu wani mutum da ke cikin hankalinsa da zai je yana kashe-kashen bayin Allah bisa ko wani hujja.”

KU KARANTA KUMA: Yan bindiga sun halaka wani hazikin sojan sama a Kaduna (hoto)

Basaraken ya kuma zargi yan siyasa da rura wutar rikicin, inda ya roki yan Najeriya da kada su bari a mayar da su karen farauta, jaridar The Cable ta ruwaito.

Ya zama dole a dakatar da wannan haukan – Sultan ya yi magana kan kashe-kashen kudancin Kaduna
Ya zama dole a dakatar da wannan haukan – Sultan ya yi magana kan kashe-kashen kudancin Kaduna
Source: UGC

“Idan kuka ci gaba da rura wutar kashe-kashen saboda banbanci kabila ko addini toh bayin Allah ake kashewa yayinda ake kare masu mulki” in ji shi.

Nasir El-Rufai, gwamnan jihar Kaduna, ya ce rikicin kudancin Kaduna ya samo asali tun rikicin Kasuwan Magani na farko da aka yi a karamar hukumar Kajuru a 1980.

Ya ce gwamnatinsa na ta kokarin ganin ta kawo karshen kashe-kashen da dawo da zaman lafiya.

Gwamnan ya kara da cewa an samar da wani sansanin sojoji da tashar yan sandan tafi da gidanka a yankin yayinda aka tura rundunar tsaron sama yankin.

Ya ce ana amfani da kayayyaki kamar su jirage marasa matuka da na’urar gano lambar waya wajen kashe yan bindiga a jihar.

KU KARANTA KUMA: Rundunar soji ta kashe yan ta’adda 9, sun ceto mutum 7 a Gwoza

A wani labarin, rundunar Operation Accord sun kashe wasu ‘yan bindiga hudu a yankin Jeka Da Rabi da ke hanyar babbar titin Kaduna-Abuja a jihar Kaduna sannan sun samo makamai daga hannunsu.

Shugaban sashin labarai na rundunar tsaro, Manjo Janar John Enenche ne ya tabbatar da hakan a cikin wani jawabi da ya fitar a ranar Alhamis.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng