Bayan shekaru 13: Gwamna Zulum zai gudanar da zaben kananan hukumomin Borno

Bayan shekaru 13: Gwamna Zulum zai gudanar da zaben kananan hukumomin Borno

- Za a gudanar da zaben kananan hukumomi a jihar Borno cikin watan Nuwamba bayan shekaru goma sha uku

- Yawan hare-haren ta’addanci, wanda aka fara a 2009 ne ya yi sanadiyar dakatar da zaben kananan hukumomi a jihar

- Shugaban hukumar zabe mai zaman kanta a jihar Borno (BOSIEC), Alhaji Abdu Usman, ya bayyana cewa an dauki matakan da suka kamata domin zaben kananan hukuma ya gudana a ranar 28 ga watan Nuwamba

A watan Nuwamban wannan shekarar, za a gudanar da zaben kananan hukumomi, wanda rabon da a yi su a jihar Borno tun a shekarar 2007.

Hauhawan hare-haren ta’addanci, wanda aka fara a 2009 ne ya yi sanadiyar dakatar da zaben kananan hukummomi a jihar.

Shugaban hukumar zabe mai zaman kanta a jihar Borno (BOSIEC), Alhaji Abdu Usman, ya bayyana a wani taron manema labarai a Maiduguri cewa an dauki matakan da suka kamata domin zaben kananan hukumomi ya gudana a ranar 28 ga watan Nuwamba.

Bayan shekaru 13: Gwamna Zulum zai gudanar da zaben kananan hukumomin Borno
Bayan shekaru 13: Gwamna Zulum zai gudanar da zaben kananan hukumomin Borno
Asali: Twitter

Usman ya ce: “An saka ranar 28 ga watan Nuwamban 2020, domin gudanar da zaben kananan hukumomi a jihar. An shirya matakan da suka kamata tare da jerin tsare-tsaren zaben.”

A bisa ga jadawalin, hukumar ta mika takardar sanar da zaben a ranar 10 ga watan Maris kuma ya isa ga jam’iyyun siyasa a ranar 12 ga watan Maris.

Zabukan fidda ‘yan takara na jam’iyya zai gudana tsakanin 27 ga watan Agusta da kuma 21 ga watan Satumba.

KU KARANTA KUMA: A raba ni da matata Amina domin ta yi kokarin sanya mani guba – Magidanci ya sanar da kotu

Mika sunayen zababbun ‘yan takara daga jam’iyyu zai zo karshe a tsakanin 22 da 28 ga watan Satumba, da misalin 8:00 na safe zuwa 6:00 na yamma a kullun.

An kuma shirya tantance ‘yan takara a tsakanin 9 da 15 ga watan Oktoba.

Shugaban hukumar zaben ya ce za a tura jami’an zabe da kayayyakin zabe tsakanin 25 da 27 ga watan Nuwamba yayinda kamfen zai tsaya a ranar 26 ga watan Nuwamba.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng