Kashe-kashen Kudancin Kaduna: Cikakken bayani kan ganawar El-Rufai da Sultan ya bayyana

Kashe-kashen Kudancin Kaduna: Cikakken bayani kan ganawar El-Rufai da Sultan ya bayyana

- Gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya bayyana cikakken jawabi kan ganawarsa da Sultan na Sokoto

- El-Rufai ya ce basaraken ya shawarce shi kan yadda zai tabbatar da maslaha maid ore a yayinda ake tsaka da hare-hare a Kudancin Kaduna

- An kuma tattaro cewa Sultan ya nuna goyon baya kan kokarin da ake amfani da su domin kawo zaman lafiya a Kaduna

Cikakken bayani kan ganawar Gwamna Nasir El-Rufai da Sultan na Sokoto, mai martaba Muhammad Sa’ad Abubakar III, a ranar Litinin, 24 ga watan Agusta, ya bayyana.

A cewar jaridar The Nation, tattaunawar da ya gudana cikin sirri a gidan Sir Kashim Ibrahim a babbar birnin jihar tsakanin El-Rufai da basaraken ya kasance a kan kashe-kashe da ake yi a Kudancin Kaduna.

Da yake zantawa da manema labarai bayan ganawar, Sultan ya dai ce kawai ya zo ziyartar dan’uwansa ne.

Kashe-kashen Kudancin Kaduna: Cikakken bayani kan ganawar El-Rufai da Sultan ya bayyana
Kashe-kashen Kudancin Kaduna: Cikakken bayani kan ganawar El-Rufai da Sultan ya bayyana Hoto: Gwamnatin Kaduna
Asali: Twitter

Sai dai kuma, El-Rufai ya bayyana cewa basaraken arewan ya zo Kaduna ne domin shawartarsa a kan yadda zai tabbatar da zaman lafiya mai dorewa a Kudancin Kaduna biyo bayan hare-haren da ake kai wa yankin.

KU KARANTA KUMA: Ba ma rabon N45,000 a matsayin tallafin korona, in ji hukumar NCDC

A cewar gwamnan, Abubakar ya nuna farin ciki cewa addinai daban-daban da kungiyoyin kabilu a jihar ne ke bayar da dabarun wanzar da zaman lafiya a jihar.

Ya ci gaba da cewa basaraken ya basa shawarwari yayinda ya nuna goyon baya ga kokarin gwamnatin jihar wajen kawo zaman lafiya a jihar arewan.

Gwamnan ya yi addu’an cewa ziyarar Sultan zai zama mafarin zaman lafiya mai dorewa a Kudancin Kaduna.

A baya mun ji cewa kimanin sa'o'i 24 da ziyarar tsohon sarkin Kano, Sanusi Lamido Sanusi, zuwa wajen Gwamna Nasir El-Rufa'i, Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Sa'ad Abubakar III ya dira jihar Kaduna don kawo nasa ziyarar.

Mai alfarma sarkin Musulmi ya dira gidan gwamnatin Kaduna misalin karfe 12: 20 na rana a yau Litinin, 24 ga Agusta, 2020.

Ya samu tarba daga sakataren gwamnatin jihar, Balarabe Abbas; shugaban ma'aikatan El-Rufa'i, Muhammad Sani Dattijo; da kwamishinan harkokin tsaron cikin gida, Samuel Aruwan.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng