Na kan ji kunya idan na ga wasu ‘yan majalisa na bacci a zauren majalisar – Babban alkalin tarayya

Na kan ji kunya idan na ga wasu ‘yan majalisa na bacci a zauren majalisar – Babban alkalin tarayya

- Ishaq Bello, babban lauyan kotun FCT ya yi tsokai a kan cece-kuce da ke kewaye da baccin ‘yan majalisa a lokacin tattaunawa a zauren malisar

- Bello ya ce ya kan sha kunya a duk lokacin da ya ga 'yan majalisar na bacci a zauren ba tare da bayar da kowani gudunmawa ba a lokacin zantawa

- Ya bayyana cewa akwai bukatar matasa masu jini a jika su fito su kawo canjin da ake bukata a fadin kasar

Babban alkalin babbar kotun birnin tarayya (FCT), Ishaq Bello ya yi tsokai a kan cece-kuce da ke kewaye da baccin ‘yan majalisa a lokacin zaman al’ada a zauren majalisar.

Bello ya bayar da tabbacin cewa akwai bukatar matasa masu jini a jika su fito su kawo canjin da ake bukata a fadin kasar.

Ya bayyana hakan ne a wani taron kara ma juna sani da aka shirya ma lauyoyi masu tasowa a ranar Litinin, 24 ga watan Agusta, shafin Linda Ikeji ya ruwaito.

Na kan ji kunya idan na ga wasu ‘yan majalisa na bacci a zauren majalisar – Babban alkalin tarayya
Na kan ji kunya idan na ga wasu ‘yan majalisa na bacci a zauren majalisar – Babban alkalin tarayya
Asali: Facebook

Babban alkalin ya bayyana cewa ya kan sha kunya a duk lokacin da ya ga ‘yan majalisa na bacci a yayin zamansu.

KU KARANTA KUMA: Najeriya na neman hakkin danta, Ibrahim Khaleel Bello wanda aka kashe a kasar Cyprus

Ya ce: “Idan na ga mutane masu yawan shekaru na bacci a majalisar dattawa ko majalisar wakilai, ba tare da suna bayar da kowani irin gudunmawa ba alhalin suna da matasa masu jini a jika a mazabunsu da za su inganta, na kan ji kunya.”

Kan rikicin da ya kunno kai a kungiyar lauyoyin Najeriya (NBA), biyo bayan zaben Olumide Akpata, wanda ba babban lauya (SAN) bane a matsayin shugabanta, Bello ya bukaci manyan lauyoyi da su amshi sakamakon zaben hannu bibbiyu.

A wani labari na daban, majalisar Wakilai ta yi barazanar yin karar Ministan Niger Delta Godswill Akpabio a kotu kan ikirarin da ya yi na cewa kaso mai yawa cikin kwangilolin hukumar NDDC, yan majalisan ne aka bawa.

Ministan ya yi wannan ikirarin ne yayin da ya bayyana a gaban kwamitin majalisar da aka kafa domin duba kudaden da ake kashewa a hukumar ta NDDC da ake ganin ya wuce hankali.

Daily Trust ta ruwaito cewa Majalisar, a zaman ta na ranar Talata, ta kallubalanci ministan ya wallafa sunayen yan majalisar da ya yi ikirarin sun karbi kwangilar a NDDC.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng