Kungiyar ISWAP ta yi garkuwa da mutane masu dimbin yawa a Borno
Wasu da ake zargin 'yan kungiyar ta'addanci ta Islamic State of West Africa Province (ISWAP) ne sun sace daruruwan mutane sunyi garkuwa da su a jihar Borno kamar yadda AFP ta ruwaito.
Rahotanni sun bayyana cewa 'yan ta'addan masu alaka da kungiyar, a daren jiya Talata sun kai hari a Kukawa da ke Tafkin Chadi inda suka sace mutane masu yawa da suka dawo gidajensu bayan shafe shakaru biyu a sansanin yan gudun hijira a cewar Babakura Kolo, shugaban yan sa kai na yankin.

Asali: Twitter
DUBA WANNAN: Shugaban kasar Portugal ya fada cikin ruwa ya ceto mata biyu (Hotuna)
A watan Yuni, a kalla sojoji 20 da farar hula fiye da 40 ne suka riga mu gidan gaskiya sakamakon wasu hare hare biyu da 'yan kungiyar suka kai kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.
Kazalika, yan kungiyar ta'addancin sun kashe a kalla mutum 81 a wani hari da suka kai a wani kauye da ke karamar hukumar Gobiyo a jihar Borno a watannin baya.
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng