Buhari ya aika sakon gaisuwa ga Babangida yayinda ya cika shekaru 79 a duniya

Buhari ya aika sakon gaisuwa ga Babangida yayinda ya cika shekaru 79 a duniya

- Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bi sahun sauran ‘yan Najeriya waje taya Ibrahim Babangida wanda ya cika shekaru 79 murna

- A wani sakon taya murna, Buhari ya ce za a dunga tuna aikin a Babangida ya yi wa Najeriya a koda yaushe

- Shugaban kasar ya yi adu’an Allah ya kara wa tsohon Shugaban kasar lafiya da nisan kwana

Shugaban kasa Muhammadu Buhari a ranar Lahadi, 16 ga watan Agusta, ya bi sahun ‘yan Najeriya wajen taya tsohon shugaban kasa a mulkin soja, Ibrahim Babangida, wanda ya cika shekaru 79 a duniya murna.

A wani sakon taya murna da kakakinsa, Femi Adesina ya saki, Buhari ya bayyana cewa a kullun ‘yan Najeriya za su dunga tuna kyawawan ayyukan Babangida.

Buhari ya aika sakon gaisuwa ga Babangida yayinda ya cika shekaru 79 a duniya
Buhari ya aika sakon gaisuwa ga Babangida yayinda ya cika shekaru 79 a duniya Hoto: Daily Post
Asali: UGC

Sakon ya zo kamar haka: “Yayinda tsohon shugaban kasa a mulkin soja ya kara sabon shekara, Shugaban kasar ya yi amanna cewa kasar za ta dunga tunawa da ayyukansa a koda yaushe.

“Shugaba Buhari na addu’a ga Allah a kan ya ci gaba da kara wa Janar Babangida karfi, ya kara masa lafiya da tsawon rai."

An haifi tsohon Shugaban kasa a mulkin soja, Babangida a ranar 17 ga watan Agusta, 1941 sannan ya yi shugabanci tsakanin 1985 da 1993.

Tsohon janar din mai ritaya ya yi aiki a matsayin Shugaban rundunar sojin kasar kafin ya zama Shugaban kasa daga Janairun 1984 zuwa Agustan 1985.

KU KARANTA KUMA: Mazauna Abuja sun koka a kan yawan sace-sacen mutane

Wikipedia ta ruwaito cewa Babangida ya rike mukamai a rundunar soji sannan ya yi yaki a lokacin yakin basasan Najeriya.

Babangida wanda ya kasancce haifafan Minna, jihar Neja ya shiga rundunar sojin Najeriya a ranar 10 ga watan Disamba, 1962, bayan ya halarci makarantar kwalejin horon soji, wanda ke Kaduna.

A wani labari na daban, IBB ya yi martani a kan rahoton da ake yadawa wanda ke ikirarin cewa yana neman matar aure.

A yayin da aka tambayesa a wata tattaunawa da aka yi da shi idan da gaske ne yana neman matar aure, tsohon shugaban kasar ya ce: "hakan kafafen yada labarai ke so. Mutane da dama suna tambayata gaskiyar lamarin."

Tun bayan rasuwar Maryam Babangida a 2009, tsohon shugaban kasar bai sake yin aure ba sai dai zama da yake yi da 'ya'yansa.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng