WAEC: Ganduje ya yi afuwa ga daliban kwaleji da suka yi mishi zanga-zanga
- Gwamna Abdullahi Umar Ganduje, ya bada umarnin gafara ga dukkan daliban da suka shiga zanga-zangar da aka yi a kwalejin kimiyya na Dawakin Tofa da ke jihar Kano
- Ganduje ya yi masu afuwan ne domin yan aji shida su samu damar zana jarrabawar WAEC
- Gwamnan ya kara da jan kunnen daliban da su kasance masu bin doka don tabbatar da cewa irin wannan lamarin bai sake faruwa ba a makarantar duk rintsi
Gwamnan jihar Kano, Dr. Abdullahi Umar Ganduje, ya bada umarnin gafara ga dukkan daliban da suka shiga zanga-zangar da aka yi a kwalejin kimiyya na Dawakin Tofa da ke jihar Kano.
A wata takardar da Lauratu Ado Diso, babbar sakatariyar ma'aikatar ilimi ta jihar Kano ta sa hannu a ranar Alhamis, ta ce Gwamnan ya bai wa ma'aikatar ilimi ta jihar umarnin.
Ya ce a dawo da daliban aji shida na makarantar domin su rubuta jarabawar kammala sakandire, jaridar Sun ta ruwaito.

Asali: UGC
Wannan takardar ta fita ne dauke da kwanan wata 12 ga watan Augustan 2020, bayan an mika takardar ga kwamishinan ilimi na jihar, Muhammadu Sanusi S. Kiru, kafin a fara taron majalisar zartarwa ta jihar.
A takardar, gwamnan ya kara da jan kunnen daliban da su kasance masu bin doka don tabbatar da cewa irin wannan lamarin bai sake faruwa ba a makarantar duk rintsi.
An shawarci iyayen da suka biya wa yaran kudin jarabawar a makarantar da su gaggauta dawo da yaran kwalejin don fara shirin jarabawar, wacce za a fada a ranar 17 ga watan Augustan 2020.
KU KARANTA KUMA: Lukman ya fallasa wani sirri da zagon kasa a jam'iyyar APC
Wani mahaifi na daya daga cikin daliban, wanda ya bukaci a boye sunansa, ya nuna farin cikinsa yayin da ya tabbatar da cewa 'ya'yansu sun koyi darasi daga kuskurensu.
A gefe guda, hukumar shirya jarrabawar makarantun sakadandare ta Najeriya, NECO, ta fitar da jadawalin jarrabawar shekarar 2020 da ka'idojin rubuta jarrabawar ta bana.
Hakan na zuwa ne a lokacin da hukumar jarrabawar ta bayyana cewa za ta saka naurar daukan bidiyon sirri na CCTV a dakunan rubuta jarrabawar domin hana magudi.
Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng