Saudiyya: Wani bawan Allah zai kai matarsa kotu don ta yi masa leken asiri a WhatsApp

Saudiyya: Wani bawan Allah zai kai matarsa kotu don ta yi masa leken asiri a WhatsApp

- Wani magidanci a kasar Saudiyya na shirin kai matarsa kotu don ta yi masa leken asiri a WhatsApp

- Ya ce ta shafe tsawon wata tara tana kutse a WhatsApp dinsa sannan tana ganin dukkan sakonni da bidiyo da aka turo masa babu saninsa

- A bangaren matar kuwa, ta bukaci ya sauwake mata igiyoyin aurensa da ke kanta kuma ya gayyaci kudin tallafin da zai hada mata da takardarta

Wani bawan Allah a kasar Saudiyya na yunkurin kai matarsa gaban kuliya a kan leken asirin da take masa a kan sakwanninsa na manhajar WhatsApp na tsawon wata tara.

Kamar yadda jaridar Saudi Gazette ta wallafa, mutumin ya gane cewa matarsa wacce malamar makaranta ce, tana kutse a WhatsApp dinsa sannan tana ganin dukkan sakonni da bidiyo da aka turo masa babu saninsa.

Saudiyya: Wani bawan Allah zai kai matarsa kotu don ta yi masa leken asiri a WhatsApp
Saudiyya: Wani bawan Allah zai kai matarsa kotu don ta yi masa leken asiri a WhatsApp Hoto: BBC Hausa
Asali: UGC

Kamar yadda yace, abin da matarsa ta aikata masa laifi ne babba kuma zamba ne na yanar gizo.

A bangaren matar kuwa, ta bukaci ya sauwake mata igiyoyin aurensa da ke kanta kuma ya gayyaci kudin tallafin da zai hada mata da takardarta.

A yayin da aka tuntubi mata, ba tace komai a kan batun ba. Sai dai ta tabbatar da cewa ta nemi a raba auren saboda bata son bayyana sirrin aurensu ga jama'a.

KU KARANTA KUMA: Gwarzo: Wani matashi ya aura mata biyu a lokaci daya kuma rana daya (Hotuna)

A wani bangare kuwa, wata kwararriya a harkar tsaron yanar gizo ta yi gargadi a kan amfani da Wi-Fi na kyauta da ake samu a filayen jiragen sama da otel.

Ta ce za a iya yi wa mutum kutsen sirri a hakan.

A wani labari na daban, wata Baiwar Allah da ke yankin Embakasi ta rabu da mijinta bayan tsawon shekaru su na zaman aure a sakamakon kama shi da ta yi da laifin yaudara.

Shamin ta shafe shekaru kimanin goma tare da maigidanta, ta na zaton ya na aiki ne a babban filin tashi da saukar jiragen sama na Jomo Kenyatta a kasar Kenya.

A wata hira da ta yi da Anthony Ndiema a filin Nisamehe a wata tashar talabijin a kasar Kenya, Shamim ta ce sai daga baya ta samu labarin inda mijinta ya ke aiki.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel