Saudiyya: Wani bawan Allah zai kai matarsa kotu don ta yi masa leken asiri a WhatsApp

Saudiyya: Wani bawan Allah zai kai matarsa kotu don ta yi masa leken asiri a WhatsApp

- Wani magidanci a kasar Saudiyya na shirin kai matarsa kotu don ta yi masa leken asiri a WhatsApp

- Ya ce ta shafe tsawon wata tara tana kutse a WhatsApp dinsa sannan tana ganin dukkan sakonni da bidiyo da aka turo masa babu saninsa

- A bangaren matar kuwa, ta bukaci ya sauwake mata igiyoyin aurensa da ke kanta kuma ya gayyaci kudin tallafin da zai hada mata da takardarta

Wani bawan Allah a kasar Saudiyya na yunkurin kai matarsa gaban kuliya a kan leken asirin da take masa a kan sakwanninsa na manhajar WhatsApp na tsawon wata tara.

Kamar yadda jaridar Saudi Gazette ta wallafa, mutumin ya gane cewa matarsa wacce malamar makaranta ce, tana kutse a WhatsApp dinsa sannan tana ganin dukkan sakonni da bidiyo da aka turo masa babu saninsa.

Saudiyya: Wani bawan Allah zai kai matarsa kotu don ta yi masa leken asiri a WhatsApp
Saudiyya: Wani bawan Allah zai kai matarsa kotu don ta yi masa leken asiri a WhatsApp Hoto: BBC Hausa
Asali: UGC

Kamar yadda yace, abin da matarsa ta aikata masa laifi ne babba kuma zamba ne na yanar gizo.

A bangaren matar kuwa, ta bukaci ya sauwake mata igiyoyin aurensa da ke kanta kuma ya gayyaci kudin tallafin da zai hada mata da takardarta.

A yayin da aka tuntubi mata, ba tace komai a kan batun ba. Sai dai ta tabbatar da cewa ta nemi a raba auren saboda bata son bayyana sirrin aurensu ga jama'a.

KU KARANTA KUMA: Gwarzo: Wani matashi ya aura mata biyu a lokaci daya kuma rana daya (Hotuna)

A wani bangare kuwa, wata kwararriya a harkar tsaron yanar gizo ta yi gargadi a kan amfani da Wi-Fi na kyauta da ake samu a filayen jiragen sama da otel.

Ta ce za a iya yi wa mutum kutsen sirri a hakan.

A wani labari na daban, wata Baiwar Allah da ke yankin Embakasi ta rabu da mijinta bayan tsawon shekaru su na zaman aure a sakamakon kama shi da ta yi da laifin yaudara.

Shamin ta shafe shekaru kimanin goma tare da maigidanta, ta na zaton ya na aiki ne a babban filin tashi da saukar jiragen sama na Jomo Kenyatta a kasar Kenya.

A wata hira da ta yi da Anthony Ndiema a filin Nisamehe a wata tashar talabijin a kasar Kenya, Shamim ta ce sai daga baya ta samu labarin inda mijinta ya ke aiki.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng