EFCC: An fara zargin Hukuma da yi wa manyan Ma’aikata cin layi a aiki

EFCC: An fara zargin Hukuma da yi wa manyan Ma’aikata cin layi a aiki

Bincike na musamman da jaridar The Cable ta yi, ya nuna cewa akwai zargin cin layi da ake yi a hukumar EFCC mai yaki da masu yi wa tattalin Najeriya zagon-kasa.

Jaridar ta ce an tura wasu daga cikin jami’an hukumar EFCC su rike manyan ofisoshi na shiyyoyi da ake da su a fadin kasar nan duk da cewa akwai wadanda su ka sha gabansu.

Wannan mataki da EFCC ta dauka bai yi wa manyan ma’aikatan hukumar dadi ba. Abin da hakan ya ke nufi shi ne za a samu jami’an da ke daukar umarni daga wurin yaransu.

Sabon mukaddashin shugaban EFCC na kasa, Mohammed Umar ne ya yi nadin mukaman da ya bar wasu jami’ai su na ta faman guna-guni kamar yadda rahoton ya bayyana.

A wata takarda da ta fito daga hukumar EFCC ta shiga hannun jaridar, an ga cewa Mohammed Umar ya sauyawa ma’aikata 37 wurin aiki, daga ciki akwai manyan jami’ai 20.

Binciken da aka yi, ya nuna cewa wasu daga cikin wadannan ma’aikata 20 da aka zaba za su rike ofisoshin shiyyoyi ne, yayin da wasunsu kuma za su zama mataimakansu.

Sabon shugaban na EFCC, mataimakin kwamishinan ‘yan sanda ne kuma darekta kafin yanzu.

Mafi yawan wadanda aka ba wannan aiki su na kan mukamin PDS, DCDS, CSP da kuma ACP ne. PDS shi ne mataki na babban mai bincike, DCDS shi ne mai bi masa a aiki.

Umar ya umarci wadanda aka ba mukami su yi maza su soma aiki ba tare da jiran wata-wata ba.

Wani ma’aikacin hukumar EFCC ya shaidawa jaridar a boye cewa wannan nadin mukamai da aka yi kwanan nan, ya sabawa yadda aka san hukumar kasar da rabon aiki.

“Sababbin nadin mukaman da aka yi ya fito kwanan nan, sai a dauki ma’aikacin da ke kan matakin aiki na 12 ko 13, ace zai jagoranci jami’in da ya kai mataki na 16 a babban ofis.”

Majiyar ya koka da yadda ake so babba ya dauki umarni wurin yaronsa. Ya ce: “A bangaren shari’a, an daina aiki. Dole sai an shawo kan wannan matsala, babu adalci a haka.”

KU KARANTA: Magu ya kare kansa daga zargin facaka da dukiyar Gwamnati

EFCC: An fara zargin Hukuma da yi wa manyan Ma’aikata cin layi a aiki
An dakatar da Ibrahim Magu Hoto: Twitter/EFCCNigeria
Asali: UGC

Jami’in ya ke cewa: “EFCC ce kawai hukumar da babba ya ke daukar umarni daga karami.”

Ga jerin jami’an da aka yi wa sauyin wurin-aiki:

1. Baba Mallam

2. Daniel O

3. Itam Obono

4. Babalola Johnson

5. Hadjia Mohammed

6. Chukkol Abdulkareem

7. Onwukwe Obiora

8. Mukhtar Bello

9. Ozugha Innocent

10. Edeh Uchenna

11. Oseni Kazeem

12. Bawa Kaltungo

13. Kumo Modibbo

14. Ringim Hauwa

15. Akogwu Eleojo

16. Amusan Kolawole

17. Abdullahi Lana

18. Adebayo Adeniyi

19. Oshodi Johnson

20. Akinroyeje Toyosi

21. Mualledi Dogondaji

22. Bawa Saidu

23. Aliyu Nuhu

24. Abdulrasheed Ahmed

25. Usman Muktar

26. Ahuchogu Austen

27. Ishaya Dauda

28. Usman Sambo

29. Ajani Aminat

30. Mohammed Sanusi

31. Thomas Kadiri

32. Abdullahi Sanusi

33. Ahmad Sabir

34. Rilwan Hamzat

35. Bamisaye Oyedele

36. Ahmed Usman

Idan ku na da wata shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Asali: Legit.ng

Online view pixel