Borno ta dauki 35% na kashe-kashen da aka yi a rabin shekarar bana

Borno ta dauki 35% na kashe-kashen da aka yi a rabin shekarar bana

Alkaluman da Nigeria Security Tracker da CFR ta fitar ya bayyana cewa mutane sama da 5, 600 su ka mutu a watanni shida na farkon shekarar nan.

Kamfanin StatiSense da su ka saba tara alkaluma na kasashen Duniya sun ce an rasa wadannan mutane a Najeriya ne daga farkon Junairu zuwa watan Yuli.

Kamar yadda alkaluman su ka nuna, jihar Borno ta dauki akalla 35% na kason kashe-kashen da aka yi a wannan lokaci. Jihar ta rasa rayukan fiye da mutum 2, 000.

Legit.ng ta lura cewa jihohi 12 na farko da aka fi fama da kashe-kashe, duk sun fito ne daga yankin Arewacin kasar.

Jihohin Kudancin Najeriya biyar kacal ne su ka fito a cikin sahun 20 na farko. Jihohin su ne: Delta, Ribas, Edo, Bayelsa da kuma Kuros-Riba inda aka rasa rayuka 215.

A shekarar nan babu jihar da ba a samu kashe-kashe ba. Jihar farko da ta fito a wannan mummunan sahu daga Kudancin Najeriya ita ce Delta a yankin Neja-Delta.

KU KARANTA: Sanatoci sun dage a kan maganar sauke Hafsun Sojojin Najeriya

Borno ta dauki 35% na kashe-kashen da aka yi a rabin shekarar bana
Shugaban kasa Buhari Hoto: Fadar Shugaban kasa
Asali: Twitter

Jihar da ta samu karancin adadi ita ce Kebbi inda mutum daya aka rasa a sanadiyyar kashe-kashe a tsawon watanni shida.

Sauran fitattun jihohin da ba a samu kashe-kashe su ne Bauchi, Kwara, Jigawa, Kano da birnin tarayya Abuja. A Kano rayuka biyu kacal aka rasa zuwa yanzu.

Ga yadda jerin ya ke:

Borno: 2,038

Kaduna: 730

Zamfara: 727

Katsina: 565

Benue: 161

Yobe: 149

Taraba: 135

Niger: 130

Adamawa: 119

Sokoto: 111

Filato: 110

Kogi: 88

Delta: 67

Ribas: 51

Edo: 48

Legass: 43

Oyo: 32

Anambra: 30

Bayelsa: 30

Kuros Riba: 30

Ebonyi: 28

Nassarawa: 27

Ondo: 24

Ogun: 23

Habuja: 20

Imo: 16

Abia: 12

Akwa Ibom: 11

Bauchi: 11

Kwara: 8

Osun: 7

Enugu: 6

Jigawa: 6

Ekiti: 4

Kano: 2

Kebbi: 1

(Alkaluma daga: Nigeria Security Tracker / CFR)

Kafin yanzu kun ji cewa Shugaba Hassan Rouhani zai taimakawa kasar Lebanon da kayan magani bayan abin da ya faru a garin Bierut.

Idan ku na da wata shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Asali: Legit.ng

Online view pixel