An sanar da rasuwar tsohon Gwamnan Jihar Ondo Bamidele Olumilua

An sanar da rasuwar tsohon Gwamnan Jihar Ondo Bamidele Olumilua

- Tsohon gwamna Bamidele Olumilua ya cika ya na da shekara 80

- Tsohon gwamnan Ondon ya mutu ne a gidansa da ke jihar Ekiti

- Bamidele Olumilua ya yi mulki tsakanin shekarar 1992 da 1993

Cif Bamidele Olumilua, wanda ya yi mulki a tsohuwar jihar Ondo ya rasu. Marigayin ya bar Duniya ya na da shekaru kimanin 80 da haihuwa.

Bamidele Olumilua shi ne gwamna na goma a jeringiyar wadanda su ka yi mulki a Ondo. Olumilua ya mulki jihar ne tsakanin 1992 da 1993.

Kamar yadda mu ka samu labari, jaridar The Tribune ce ta fara fitar da rahoton mutuwar wannan dattijon ‘dan siyasan a yau 4 ga watan Yuni, 2020.

Babban ‘Dan marigayin, Muyiwa Olumilua ya bada sanarwar mutuwar tsohon. Olumilua kwamishina ne na watsa labarai a gwamnatin Ekiti.

KU KARANTA: Hukumar 'Yan Sanda ta PSC ta rasa wani daga cikin Jami'an ta

An sanar da rasuwar tsohon Gwamnan Jihar Ondo Bamidele Olumilua
Bamidele Olumilua Hoto: Daily Post
Asali: UGC

Kwamishinan yada labarai da ziyarar buda ido na gwamnatin Fayemi ya bayyana cewa mahaifin na su ya mutu ne a farkon yau Alhamis a gida a Ekiti.

Cif Olumilua ya na cikin wadanda su ka lashe zaben da gwamnatin sojan Janar Ibrahim Badamasi Babangida ta shirya a farkon shekarar 1992.

Olumilua ya dare mulki ne a karkashin jam’iyyar SDP inda ya doke ‘dan takarar NRC. A shekarar 1993 ne Janar Sani Abacha ya sauke duka gwamnoni.

Olumilua ya karbi mulki ne a hannun Sunday Abiodun Olukoya. Bayan gajeren wa’adin da ya yi, ya dawo siyasa a 1999 inda ya shiga jam’iyyar PDP.

Marigayin ya rike mukami a gwamnatin jam’iyyar PDP, amma daga baya ya sauya-sheka. Kafin rasuwarsa, jam’iyyar siyasar karshe da ya yi ita ce AC.

KU KARANTA: Yadda za ka rika samun labaran Legit.ng Hausa a shafinka

Idan ku na da wata shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Asali: Legit.ng

Online view pixel