Duk mamban da ya karba mukami daga PDP, ya bar jam'iyya - APC ta ja kunnen mambobinta

Duk mamban da ya karba mukami daga PDP, ya bar jam'iyya - APC ta ja kunnen mambobinta

Jam'iyyar APC reshen jihar Adamawa ta ce duk dan jam'iyyar da ya karbi mukami daga Gwamna Fintiri za a yi mishi korar kare daga jam'iyyar.

Gwamna Ahmadu Fintiri dan jam'iyyar PDP ne wanda cikin kwanakin nan ya nada masu bada shawara, hadimai na musamman tare da shugabannin cibiyoyi. A saboda haka ne gwamnan ya nada wasu daga cikin 'yan jam'iyyar APC.

Amma a wata takarda da jam'iyyar APC ta fitar a ranar Laraba da hannun sakataren yada labarai na jam'iyyar, Mohammed Abdullahi, ya jaddada cewa duk mamban da ya karba wani mukami daga PDP za a kore shi daga jam'iyya.

Duk mamban da ya karba mukami daga PDP, ya bar jam'iyya - APC ta ja kunnen mambobinta
Duk mamban da ya karba mukami daga PDP, ya bar jam'iyya - APC ta ja kunnen mambobinta Hoto: Premium Times
Asali: UGC

Jam'iyyar ta ce, "Mun duba nade-naden da gwamnatin PDP tayi a jihar Adamawa amma mun hango sunayen wasu mambobin jam'iyyar mu.

"Muna son janyo hankalin 'yan jam'iyyar da aka nada a kan cewa duk wanda ya karba nadi daga wata jam'iyya da ba APC ba ya bar jam'iyyar.

"A yayin da muke jinjinawa 'yan jam'iyyar a kan gaskiyarsu da rikon amana yayin da suka yi watsi da nadin, duk wanda ya karba ha bar jam'iyyar mu gaba daya."

Jam'iyyar ta zargin gwamnatin da yunkurin hargitsa APC.

Ta ce, "A tsanake APC ke kallon kokarin jam'iyyar PDP na hargitsa hadin kan da ke APC. Wannan abun ba zai yuwu ba kuma har abada ba zai yuwu ba.

"A don haka muke kira ga 'ya'yan jam'iyyar mu da su mayar da hankali wajen goyon bayan mulkin shugaban kasa Muhammadu Buhari a yayin da muke fatan karbar mulkin Adamawa a 2023."

KU KARANTA KUMA: Covid-19: Jihohi 4 da suka yi watsi da umarnin FG na bude wuraren bauta

A wani labari na daban, mun ji cewa rikicin da ya barke a jam’iyyar APC ta reshen jihar Neja ya kai intaha bayan an kai ga cafke shugaban jam’iyyar mai-mulki.

Jaridar ta ce an kama Injiniya Mohammad Jubrin Imam a farkon makon nan, inda ake zarginsa da laifin cin kudin jam’iyyarsa.

Rahotanni sun ce kawo yanzu dai an saki shugaban. An cafke Jubrin Imam ne a ranar Talata, 2 ga watan Yuni, 2020.

An kuma sake shi ne a yau Laraba. Sakataren yada labarai na jam’iyyar APC a jihar Neja ya tabbatar da wannan.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng