Manyan kabilu 10 da suka fi shahara a nahiyar Afrika

Manyan kabilu 10 da suka fi shahara a nahiyar Afrika

Ubangiji ya albarkaci nahiyar Afrika da mutane hazaikai da kuma kabilu masu tarin yawa.

Legit.ng ta tattara muku kabilu daban-daban da suka fi jama’a masu tarin yawa a nahiyar Afrika.

Ga jerin kabilu 10 a nahiyar Afrika da suka fi kowacce kabila yawa kamar yadda Facts one ta bayyana.

1. Kabilar Hausa - miliyan 78:

Tana da mutane a kalla miliyan 78 a fadin nahiyar Afrika. Ana samu masu yin yaren a kasashe masu tarin yawa na fadin haiyar.

2. Igbo - miliyan 45:

Da mutum miliyan 45 ne kabilar Ibo ta zama ta biyu a cikin kabilu mafi yawan mutane a nahiyar Afrika.

3. Yoruba - miliyan 44:

Kabilar nan ce ke biye da kabilar Ibo a yawan mutane a nahiyar Afrika. Tana da mutane masu yawan miliyan 44.

4. Oromo - miliyan 40:

Kabilar Oromo ce kabila ta hudu a yawan jama’a a nahiyar Afrika. Tana da mutum miliyan 40.

5. Fulani - miliyan 35:

Kabilar Fulani ce ta biyar a wannan jerin, tana da mutane miliyan 35 a nahiyar Afrika.

6. Amhara - miliyan 20.2:

Kabilar ce ta shida a wannan jerin kuma tana da jama’a miliyan 20.2

7. Akan - miliyan 20:

Akan kabila ce da ke da yawan mutane har miliyan 20 a fadin nahiyar Afrika.

8. Somali - miliyan 20:

Kabilar Somali c eke biye da Akan wacce ke da miliyan 20 na jama’a.

9. Hutu - miliyan 18.5:

Kabilar tana da jama’a miliyan 18.5 na masu yin yarenta a Afrika.

10. Ijaw - miliyan 15:

Kabilar Ijaw ce ta karshe kuma ta goma a wannan jerin. Tana da mutane miliyan 15 da ke yin yaren a Afrika.

KU KARANTA KUMA: Buhari ya yi garambawul a rundunar 'yan sanda, ya kirkiri sabbin kwamand 5

A baya mun kawo cewa, yaren Hausa ne yaren da aka fi yi kuma mafi dadewa a cikin yankin mutane miliyan 120 kamar yadda aka gano.

Masu yin yaren na nan dankam a kasashen Najeriya, Nijar, Chadi, jamhuriyar Benin, Kamaru, Togo, jamhuriyar Afrika ta tsakiya, Ghana, Sudan, Eritrea, Guinea, Gabon, Senegal da Gambia.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel