Sabbin mutane 108 sun sake kamuwa da kwayar cutar covid-19 a Najeriya, jimilla 981

Sabbin mutane 108 sun sake kamuwa da kwayar cutar covid-19 a Najeriya, jimilla 981

An samu karin sabbin mutane 108 da su ka kamu da kwayar cutar coronavirus a ranar Alhamis, kamar yadda hukumar shawo kan cututtaka ma su yaduwa ta kasa (NCDC) ta sanar.

Jimillar mutanen da aka tabbatar su na dauke da kwayar cutar a Najeriya ya zama 981.

A cewar NCDC, mutum 78 ne su ka kamu da kwayar cutar a Legas, 14 a Abuja, da mutum 5 a jihar Ogun.

An tabbatar da samun mutum 4 a jihar Gombe, karin mutum 3 a jihar Borno da mutum biyu a jihar Akwa Ibom. An samun mutum dai - dai a jihohin Kwara da Filato.

Ya zuwa yanzu annobar cutar covid-19 ta hallaka mutane 31 a Najeriya, yayin da aka sallami mutum 197 bayan an tabbatar da warkewarsu.

Ga jerin jihohi da adadin mutanen da aka tabbatar sun kamu da cutar covid-19 ya zuwa yanzu;

Lagos-582

FCT-133

Kano-73

Ogun-29

Katsina-21

Osun-20

Oyo-17

Edo-17

Borno-12

Kwara-11

Akwa Ibom-11

Kaduna-9

Gombe-9

Bauchi-8

Delta-6

Ekiti-4

Ondo-3

Rivers-3

Jigawa-2

Enugu-2

Niger-2

Abia-2

Benue-1

Anambra-1

Sokoto-1

Adamawa-1

Plateau-1

Legit.ng ta wallafa cewa shugaban kasa, Muhammadu Buhari, ya aika sakon fatan alheri ga dukkan Musulman Najeriya da na duniya baki daya a yayin da za su fara azumin kwana 30, biyo bayan ganin watan Ramadan.

DUBA WANNAN: Gwamnan PDP ya bayar da umarnin yin bulala ga duk wanda aka gani babu takunkumi a jiharsa

"Ina taya duk Musulmi muranar zuwan azumin watan Ramadan, watan rahama, jin kai da taimakon mabukata," a cewar Buhari, kamar yadda kakakinsa, Mallam Garba Shehu, ya fada.

Shugaba Buhari ya bayyana azumin shekarar 2020 a matsayin mai cike da kalubale, saboda ya zo a cikin annobar da ta yadu zuwa kasashen duniya 200, lamarin da ya sa kasashe daukan tsauraran matakai.

A cewar shugaba Buhari, kusan duk kasashen duniya sun shawarci jama'arsu a kan su kauracewa taron jama'a da yawa, su gudanar da salloli da addu'o'i a gidajensu.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel