Gwamnati za ta rage Biliyan 25 daga kasafin Majalisa saboda cutar COVID-19

Gwamnati za ta rage Biliyan 25 daga kasafin Majalisa saboda cutar COVID-19

Za a sake duba kasafin kudin majalisar tarayyar Najeriya na wannan shekara, inda ake tunanin gwamnatin tarayya za ta rage Naira biliyan 25.6 daga cikin kudinta.

Gwamnatin Najeriya ta dauki wannan mataki ne bayan annobar COVID-19 ta jawo rugurgujewar farashin mai a Duniya, inda mai ya rage daraja a kasuwa da fiye da 60%.

Jaridar Daily Trust ta bayyana cewa zaftare N25 daga cikin kasafin kudin ‘Yan majalisa ya na nufin an rage 20% na kudin da ta yi tunanin batarwa a cikin shekarar bana.

Ita ma gwamnatin tarayya ta rage kasafin da ta yi na Naira tiriliyan 10.3. Yanzu abin da Najeriya ta ke sa ran kashewa a wannan shekara ra 2020 ya koma Naira tiriliyan 8.

Bayan ganin kudin gangar mai ya yi kasa a kasuwa, Najeriya ta dauki matakin cire 20% daga cikin kasafin ‘Yan majalisa da bangaren shari’a da kuma masu zartarwa.

KU KARANTA: Coronavirus: Babu na’urar taimakawa numfashi a wasu Jihohi

Gwamnati za ta rage Biliyan 25 daga kasafin Majalisa saboda cutar COVID-19
Annoba ta sa za a rage kudin Majalisa da Alkalai a Najeriya
Asali: Twitter

A halin yanzu za a taba kasafin shugabanni da Ministoci da ‘Yan majalisar wakilai da na dattawa da kuma masu gudanar da shari’a. Za a sanar da majalisa wannan lamari.

‘Yan majalisar tarayya sun nuna cewa a shirye su ke su sadaukar da wani kaso na kudinsu domin Najeriya ta samu damar yakar cutar Coronavirus da ke kashe Bayin Allah.

Honarabul Muhammad Tahir Monguno ya shaidawa Jaridar cewa za a rage kasafin kudin shugabannin kasar. Za a duba a ga meya kamata a cire daga kasafin bana.

Tahir Monguno ya nuna cewa za su dakatar da batun kashe Naira biliyan 37 wajen yi wa ginin majalisa kwaskwarima. Monguno ya ce kamata ya yi ayi wani abu da kudin.

Idan ku na da wata shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewa tare da mu.

Asali: Legit.ng

Online view pixel