Amurka: Sin ba ta fadan gaskiyar adadin mutanen da COVID-19 ta kashe

Amurka: Sin ba ta fadan gaskiyar adadin mutanen da COVID-19 ta kashe

Wani rahoto da ya fito daga Jaridar Bloomberg a Ranar 1 ga Watan Afrilu ya bayyana cewa kasar Sin ta boyewa Duniya hakikanin barnar da annobar Coronavirus ta yi mata.

Hukumomin leken asirin Amurka su na zargin cewa Kasar ta Sin ba ta fadin gaskiyar adadin mutanen da cutar ta kashe. Tuni an sanar da fadar Amurka game da wannan.

Binciken Amurkan ya nuna ana zargin Sin da kin fadan gaskiyar wadanda wannan cuta ta kashe, haka zalika kasar ba ta fadin gaskiya game da wadanda su ka kamu da cutar.

Har yanzu dai rahoton wannan bincike bai shiga hannun jama’a ba, amma Bloomberg ta bayyana akwai boye-boye a alkaluman kasar Sin inda cutar COVID-19 ta fara bayyana

Alkaluman kasar Sin sun bayyana cewa mutane 82, 000 ne su ka kamu da cutar, sannan kuma mutane kimanin 3, 300 sun mutu. Amurka ta na da ja da wadannan alkaluma.

KU KARANTA: Masu dauke da COVID-19 sun shigo Najeriya ta barauniyar hanya

Amurka: Sin ba ta fadan gaskiyar adadin mutanen da COVID-19 ta kashe
Kasar Sin ta na ikirarin mutane 3000 COVID-19 ta kashe tun 2019
Asali: Twitter

Kasar Amurka ta na fama da mutane fiye da 189, 000 da su ka kamu, bayan 4, 000 da cutar ta kashe. Gwamnatin Amurka ta dade ta na zargin Sin da kin fadawa kowa gaskiya.

Shugaban Amurka Donald Trump ya na zargin Sin da jawo wannan cuta. ‘Yan majalisar jam’iyya mai mulki a Amurka, sun yi tarayya a wannan ra’ayi na sukar gwamnatin Sin.

Mataimakin shugaban Amurka, Mike Pence, ya koka da yadda kasar Sin ta dade ta na kokawa da wannan cuta tun 2019 ba tare da sauran kasashe sun san halin da ake ciki ba.

Sai dai ana zargin sauran kasashe irinsu Amurka da kin bin matakan da ya kamata wajen hana yaduwar wannan cuta. Watakila wannan ya jawo cutar ta yi kamari fiye da Sin.

Bayan Sin, ana zargin wasu kasashen irinsu Iran, Rasha, Indonesiya, Masar da Saudi Arabia da musamman kasar Koriya ta Arewa da kin fadan gaskiyar tasirin wannan annoba.

Idan ku na da wata shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewa tare da mu.

Asali: Legit.ng

Authors:
Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng