Saudiyya ta sanar da warkewar mutum 66 da suka kamu da kwayar cutar COVID-19 (bidiyo)

Saudiyya ta sanar da warkewar mutum 66 da suka kamu da kwayar cutar COVID-19 (bidiyo)

A ranar Lahadi ne hukumar kasar Saudi Arabia ta sanar da cewa wasu mutane 66 da suka kamu da kwayar cutar coronavirus sun warke.

Sanarwar na kunshe ne a cikin sakon da babbar jaridar kasar Saudiyya da ake wallafa wa cikin harshen turanci; 'Saudi Gazette' ta fitar ranar Lahadi.

Akwai kimanin mutum 96 da aka tabbatar da cewa sun kamu da kwayar cutar coronavirus a kasar Saudiyya tare da asarar rayukan mutane 8.

Ya zuwa yanzu, kwayar cutar coronavirus ta kashe mutane fiye da 30,000 a fadin duniya a karshen makon nan. Kwayar cutar ta fi gigita kasar Amurka da yankin nahiyar turai a 'yan kwanakin baya bayan nan.

A ranar Lahadi ne kasar Andolus (Spain) ta sanar da mutuwar mutane 838 sakamakon kamuwa da kwayar cutar coronavirus.

DUBA WANNAN: Jerin jihohin Najeriya 12 da aka tabbatar da bullar kwayar cutar coronavirus

A wata kididdiga da jami'ar 'Johns Hopkins' ta gudanar, ta bayyana cewa mutane 30,800 ne kwayar cutar COVID-19 ta halllaka a fadin duniya, yayin da take cigaba da mamaya da karya tattalin arzikin mutane da na kasashe.

Mutane fiye da 20,000 ne kwayar cutar ta hallaka a iya yankin nahiyar turai. Kwayar cutar ta kashe mutane fiye da 1400 a rana daya a kasar Spain da Italy.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel