Mun samu labari cewa Mai martaba sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero, ya yi magana game da annobar Coronavirus wanda ta ke cigaba da girgiza Duniya.
A wani bidiyo da aka wallafa a shafin Tuwita, Mai martaba Aminu Ado Bayero ya nuna cewa ya hau kan karagar mulkin gidan dabo a wani yanayi na damuwa.
Sarkin ya na magana ne game da cutar Coronavirus da ta shiga kasashe fiye da 100. A sakamakon barkewar COVID-19, Sarki ya bukaci jama’a su yawaita addu’o’i.
Aminu Ado Bayero ya yi kira ga Mutanen Kano su tashi tsaye da addu’o’in zaman lafiya da ganin kwanciyar hankali a daidai wannan mawuyacin hali da ake ciki.
Bugu da kari, sabon Sarkin na Kano, ya bayyanawa Talakawa cewa wannan cuta wata jarrabawa ce daga Ubangiji, don haka ya bukaci a komawa Allah da roko.
KU KARANTA: Najeriya ta bukaci a kawo mata agaji game da cutar COVID-19
Sarkin ya tunatar da jama’a cewa Allah Madaukakin Sarki mai karbar addu’ar Bayinsa ne a koda yaushe don haka su dukufa babu dare ko rana wajen neman sauki.
An daura wannan bidiyo na jawabin Mai martaba ne a dandalin sada zumunta na Tuwita a Ranar Litinin, 23 ga Watan Maris, 2020 da kimanin karfe 2:00 na rana.
Yanzu haka dai gwamnatin jihar Kano ta dauki matakai na musamman domin ganin an gujewa barkewar wannan mummunar cuta da ke yawo watau COVID-19.
A daidai wannan lokaci kuma tsohon Sarki Muhammadu Sanusi II ya yi magana daga gidansa inda ya roki a daina kawo masa ziyara har sai Coronavirus ta lafa.
Idan ku na da wata shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu:
https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewa tare da mu.