Shugaban hukumar jin dadin alhazan jihar Kaduna ya mutu

Shugaban hukumar jin dadin alhazan jihar Kaduna ya mutu

Allah ya yi wa Malam Sani Dalhatu Musa, shugaban hukumar jin dadin alhazan jihar Kaduna, rasuwa a yau, Laraba.

Jaridar 'The Nation' ta rawaito cewa shugaban hukumar ya mutu ne sakamakon wani mummunan hatsarin mota da ya ritsa da shi a kan babbar hanyar Kaduna zuwa Abuja.

Malam Sani ya zama shugaban hukumar ne a watan Janairu 2020 bayan ya shafe fiye da shekaru 20 yana aiki tare da hukumar ta jin dadin alhazan jihar Kaduna.

Ya taba rike shugabancin hukumar a karamar Birnin Gwari, Igabi da sauran wasu kananan hukumomin jihar Kaduna.

Kazalika, ya taba rike mukamin shugaban aiyuka na aiyuka a hukumar kafin daga bisani ya zama shugaban aiyuka na hukumar a jihar Kaduna.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel