Yanzun nan: An yi garkuwa da babban jami'in gwamnatin Nasarawa

Yanzun nan: An yi garkuwa da babban jami'in gwamnatin Nasarawa

- Yan bindiga sun yi garkuwa da sakataren din-din-din na ma’aikatar ayyukan a jahar Nasarawa, Alhaji Jibrin Giza

- Lamarin ya afku ne a tsakar daren ranar Asabar

- Kwamishinan yan sanda a jahar, Mista Bola Longe, ya tabbatar da lamarin ga manema a Lafia

Wasu yan bindiga sun yi garkuwa da sakataren din-din-din na ma’aikatar ayyukan a jahar Nasarawa, Alhaji Jibrin Giza, a tsakar daren ranar Asabar.

Kwamishinan yan sanda a jahar, Mista Bola Longe, ya tabbatar da lamarin ga kamfanin dillancin labaran Najeriya a Lafia.

Longe ya fada ma NAN cewa yan bindiga sun sace sakataren din-din-din din daga gidansa a Shabu, wani yanki na Lafia da misalin 12:40 na tsakar dare zuwa wani wuri da ba a sani ba.

Yanzun nan: An yi garkuwa da babban jami'in gwamnatin Nasarawa
Yanzun nan: An yi garkuwa da babban jami'in gwamnatin Nasarawa
Asali: Twitter

A cewar kwamishinan yan sandan, Shugaban yan sanda a yankin ya rigada ya zuba wasu jami’ai wadanda za su bi sahun masu garkuwan da suka tsere da wadanda suka sace.

Longe ya kara da cewa ya umurci mataimakin kwamishina na ayyuka, jami’in da ke kula da rundunar yaki da fashi na musamman, da su kakkabe yankin don tabbatar da sun ceto wadanda aka sace da kuma kama masu garkuwan.

Ya kuma sha alwashin cewa rundunar ba za ta yi kasa a gwiwa ba har sai ta ceto wadanda aka sace.

Longe ya kara da cewa masu garkuwan ba su kira yan’uwan wadanda suka sace ba tukuna.

A wani labarin kuma mun ji cewa Wani sabon ango mai suna Chidubem ya saki matarsa mai suna Vivian Chidinma bayan wani tsokaci da tayi a kan yadda mata zasu kashe mazansu masu cin amana a saukake.

A wani tsokaci da Chidubem ya ga matarsa tayi a wani dandali a kafar sadarwa ta Facebook mai suna “Extraordinary mums and singles”, hankalin sabon angon ya matukar tashi.

Matar ta nuna goyon bayanta ga mata masu kashe mazansu da ke cin amanarsu.

KU KARANTA KUMA: Shekau ya yi barazanar kai ma gidan rediyon BBC, Bukarti da Minista Pantami hari

Ta shawarci matan su dau dabararta a maimakon saka wuka su kashe miji wanda hakan ke jefa su cikin babbar matsala.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng