Dahiru Bauchi da 'ya'yansa uku sun ziyarci Buhari a Villa (Hotuna, bidiyo)

Dahiru Bauchi da 'ya'yansa uku sun ziyarci Buhari a Villa (Hotuna, bidiyo)

Shugaban kasa, Muhammadu Buhari, ya karbi bakuncin babban malamin addinin Islama kuma jigo a tafiyar darikar Tijjaniyya, Sheikh Dahiru Usman Bauchi, a fadarsa, Villa, da ke Abuja a ranar Lahadi.

Babban malamin ya samu rakiyar 'ya'yansa guda uku, a cikinsu akwai Sheikh Ibrahim Dahiru Usman.

A cikin takaitaccen faifan bidiyo da hotunan da hadimin shugaban Buhari mai suna Buhari ya Sallau ya wallafa a shafinsa na Tuwita, Sheikh Bauchi ya yi wa shugaba Buhari da kasa addu'o'in samun zama lafiya da karin yalwar arziki.

A daya daga cikin hotunan da Sheikh Bauchi suka yi tare da Buhari, an ga ministan ilimi na kasa, Adamu Adamu, tare da wasu hadiman shugaban kasa.

Dahiru Bauchi da 'ya'yansa uku sun ziyarci Buhari a Villa (Hotuna, bidiyo)
Adamu Adamu, Buhari, Dahiru Bauchi da 'ya'yansa a Villa
Asali: Twitter

A wani labarin mai nasaba da Sheikh Bauchi, jikarsa, Rukayyatu Fatahu Umar ta zamo daya cikin yara Musulmai kanana a duniya da suka haddace Al-Qur'ani mai girma.

Sheikh Dahiru Usman Bauchi ne ya haifi Sayyada Maimunatu, wacce rahotanni suka bayyana cewa ita ce ta haifi Rukayyatu.

DUBA WANNAN: Buhari ya aminta da bawa masana'antun waka da fim tallafin N7bn

Karamar yarinyar ta fara haddar Qur'ani ne a wata makarantar Islamiyya da kakanta ya kafa. Makarantar kuwa na karkashin kular mahaifiyar yarinyar ne Sayyada Maimunatu.

Makarantar na nan ne a Bakin Ruwa a Kaduna.

Kamar yadda mahaifiyar yarinyar ta sanar, diyarta ta haddace littafin mai girma ne a lokacin da ta cika shekaru uku da watanni takwas a duniya.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel