Sojojin Najeriya sun kama buhun shinkafa cike da alburusai a jahar Zamfara

Sojojin Najeriya sun kama buhun shinkafa cike da alburusai a jahar Zamfara

Dakarun rundunar Sojan Najeriya dake jibge a garin Moriki na jahar Zamfara sun kama wani dan achaba dauke da buhun shinkafa wanda bincike ya fallasa ashe tarin alburusai ne makare a cikin buhun.

Jaridar Premium Times ta ruwaito majiyoyi daga rundunar Sojin Najeriya sun bayyana cewa dan Achaban ya tsere, amma an kama buhun dake dauke da alburusai 4653 samfurin 7.62mm.

KU KARANTA: Buhari ya fi kowa fahimtar matsalar tsaron da Najeriya ke fama da shi – Buratai

Sojojin Najeriya sun kama buhun shinkafa cike da alburusai a jahar Zamfara
Sojojin Najeriya sun kama buhun shinkafa cike da alburusai a jahar Zamfara
Asali: Facebook

Rahotanni sun bayyana cewa Sojojin sun kama alburusan ne bayan samun bayanan sirri dake nuna cewa ana safarar makamai zuwa Moriki, da wannan dalili suka sanya shingayen binciken ababen hawa a cikin garin.

“Mun sanya shigayen binciken ababen hawa kenan sai ga wani babur ya iso dauke da wani buhu kamar na shinkafa, amma direban babur din bai tsaya a bincike shi ba, sai muka bi shi da gudu, da ya ga zamu kure masa gudu sai ya jefar da babur din ya tsere.” Inji wani majiya daga rundunar Sojan.

Da wannan ne aka yi kira ga dakarun Soji dake yankin da suka kasance cikin shirin ko ta kwana domin yan bindiga da sauran miyagu suna cigaba da amfani sabbin dabaru daban daban domin safarar makamai da alburusai.

A wani labarin kuma, babban hafsan Sojan kasa, Laftanar Janar Tukur Yusuf Buratai ya bayyana cewa bai kamata a tunzura shugaban kasa Muhammadu Buhari wajen daukan matakin tsige manyan hafsoshin tsaro ba, saboda shi kadai ya san inda matsalar take.

A kwanakin baya ne majalisar dokokin Najeriya ta nemi Buhari ya sallamki kafatanin hafsoshin tsaron Najeriya saboda abin da suka bayyana a matsayin gazawarsu wajen kare rayukan yan Najeriya, duba da sake farfadowar da Boko Haram ta yi.

Da wannan ne babban hafsan Sojan, Laftanar Janar Tukuru Tusuf Buratai yace: “Ba tare da kalubalantar ikon majalisa ba, amma sallamar hafsoshin tsaro ba shi bane hanyar da zai warware matsalolin tsaro da Najeriya ke fama da ita.”

Buratai ya kara da cewa Buhari na sane da halin da ake ciki, kuma shi ne mai dakin, shi ya san inda ke masa yoyo, haka zalika shi kadai ne zai iya yanke hukuncin da ya kamata game da lamarin.

Ku biyo mu a https://facebook.com/legitnghausa

ko a http://twitter.com/legitnghausa

KU LATSA: Hanyar sauko da sabuwar manhajar jaridar Legit.com Hausa cikin sauki

Ga masu shawara ko korafi, a same mu a labaranhausa@corp.legit.com

Sanarwa na musamman: Shafin NAIJ Hausa ya koma Legit Hausa

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng