An yi mace-mace bayan 'Yan Boko Haram da ISWAP sun juya juna baya

An yi mace-mace bayan 'Yan Boko Haram da ISWAP sun juya juna baya

Arangama tsakanin kungiyoyin yan ta’adda biyu a yankin arewa maso gabashin Najeriya ya yi sanaiyar mutuwar mayaka da ama, wasu majiyoyi biyu suka bayyana hakan ga kafar labarai ta AFP hakan a ranar Litinin.

Mayaka a manyan motoci daga bangaren Boko Haram masu biyayya ga Abubakar Shekau sun far ma wani sansani mallakar abokan adawarsu ta ISWAP, wanda ya yi sanadiyar musayar wuta day a haddasa mutuwar wasu da dama, inji majiyar.

Mayakan na Boko Haram sun kai hari sansanin da ke kauyen Sunnawa a yankin Abadam da ke kusa da iyakar Nijar don kwato matansu da mayakan ISWAP suka kwace a harin da suka fara kaiwa sansaninsu da ke iyakar Nijar.

Jaridar Tribune ta ruwaito cewa rikicin wanda ya afku na kan bayyana a hankali-a hankali saboda karancin sabis din waya a yankin karkaran.

Da farko dai mayakan ISWAP sun kai hari wani sansanin Boko Haram a yankin Diffa da ke makwabtaka na Nijar inda suka yi garkuwa da mata 13.

KU KARANTA KUMA: Sanata Nazif ya ce babu makawa sai PDP ta kwato kujarar Shugaban kasa a 2023

Sai Boko Haram suka bibiyi matan zuwa Sunnawa a yankin tafkin Chadi wanda ke a karkashin ikon ISWAP sannan suka yanke shawarar kwato su, inji majayar. “Hakansu bata cimma ruwa ba domin har yanzu matar na a hannun wadanda suka yi garkuwa da su,” in ji shi.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng