Rundunar soji ta yi gargadi kan tashohin bincike na bogi a titin Maiduguri-Damaturu

Rundunar soji ta yi gargadi kan tashohin bincike na bogi a titin Maiduguri-Damaturu

Kwamandan Operation Lafiya Dole, Manjo Janar Olusegun Adeniyi ya karya shirunsa a kan dawowar hare-haren yan ta’addan Boko Haram a hanyar Babbar titin Maiduguri-Damaturu, ya gargadi masu ababen kan tashoshin bincike na bogi da yan ta’addan suka kafa kan babbar titin.

Kwamandan ya ci gaba da bayanin cewa kada masu ababen hawa su tsaya a kowani tashar bincike sai wanda mahukunta suka kafa a wasu wurare a hanyar, inda ya ce tashoshin bincike sahihai sune a yankunan Benisheikh, Jakana, Auno, Mainok da Njimitilo.

Manjo Janar Adeniyi ya bayyana hakan ne a wata hira da yan jarida a cibiyar rundunar Operation lafiya dole da ke Maiduguri.

Ya bayyana dawowar hare-haren yan ta’addan kan hanyar a matsayin rashin samun damar kafa cibiyarsu a kowani yanki na Najeriya.

Ya cigaba da bayyana cewa mafi akasarin wadanda yan Boko Haram suka sace ana amfani dasu ne a matsayin bayi a harkar kamo kifi da noma.

KU KARANTA KUMA:

Kwamandan ya ce daga yanzu yan ta’addan Za su dandana kudarsu a hannun rundunar sojin Najeriya idan suka cigaba da kai hare-hare a hanyar Maiduguri-Damaturu, cewa sojoji na aiki ta hanyar don kare rayuka da dukiyoyin jama’a.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng

Tags: