Yau a tarihi: 'Ghana must go' ranar da aka fitittiki mutane milyan 2 daga Najeriya

Yau a tarihi: 'Ghana must go' ranar da aka fitittiki mutane milyan 2 daga Najeriya

'Ghana Must Go' wani shahrarren kalma ne da yasamo asali a ranar 17 ga watan Junairu, 1983 inda shugaban kasan Najeriya, Shehu Shagari, ya bada umurnin fitittikan baki daga kasar.

Shagari ya bada umurnin koran dukkan baki da basu da takardun kwarai ko kuma a garkamesu.

Ya bada umurnin ne bisa ga rikicin addinin da ke faruwa a kasar a shekarar 1980 musamman a jihar Kano.

Kimanin mutane milyan biyu, maza, maata da yara aka kora daga Najeriya. Yawancinsu yan kasashen Afrika ta yamma ne musamman yan kasar Ghana. [Wikipedia]

Yau a tarihi: 'Ghana must go' ranar da aka fitittiki mutane milyan 2 daga Najeriya
Hakkin mallaka: BBC
Asali: Facebook

Ga jerin abubuwan da suka faru a rana irin ta yau:

1983: An fitittiki baki daga Najeriya

1873 Ranar da mayakan Modoc sunka samu nasara kan Sojin Amurka a yakin Modoc

1946 Kwamitin tsaro na majalisar dinkin duniya tayi ganawarta na farko

1991 Ranar da Amurka ta kai harin Bam Iraki lokacin yakin kasashen larabawa

1942 Ranar da aka haifi shahrarren da damben turawa, Muhammad Ali

KU KARANTA: Gwamna Zulum ya samu lambar yabon Musulmi mafi kokari a Najeriya, Pantami yazo na biyu

Mun kawo muku rahoton cewa a ranar 5 ga Nuwamban 2019, kungiyar masu siyar da kayan wutar lantarki ta kasar Ghana ta garkame shagunan bakin haure, ganin cewa sun take dokar kasar.

A kalla shaguna 50 na 'yan Najeriya aka garkame a Opera Square da ke tsakiyar Accra, babban birnin kasar, kamar yadda jaridar Daily Trust ta bayar da rahoto.

A makon da ya gabata ne kungiyar ta ba masu shaguna da ba 'yan kasar ba wa'adin rufe shagunansu zuwa watan Nuwamba.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng