Najeriya ce kasar da nake matukar son zuwa a rayuwata - Lil Wayne

Najeriya ce kasar da nake matukar son zuwa a rayuwata - Lil Wayne

- Sanannen tauraron hip-hop, Lil Wayne ya bayyana bukatarshi ta kawo ziyara Najeriya

- Hakan ya biyo baya ne a cikin makonni kalilan da mawakiyar gwambarar kasar Amurka, Cardi B tazo kasar

- Lil Wayne ya bayyana cewa bai taba koda zuwa nahiyar Afirka ba amma zai so zuwa Najeriya

Tauraron hip-hop, Lil Wayne ya bayyana bukatarshi ta ziyartar Najeriya.

Bukatar nan ta biyo baya ne a makonni kadan bayan da mawakiyar gambarar nan ta kasar Amurka, Cardi B ta kawo ziyara Najeriya.

Mawakin da ya karba kyautukan yabo tare da kambu daban-daban, Lil Wayne ya sanar da manema labarai ne a wani bidiyo cewa bai taba zuwa nahiyar Afirka ba.

KU KARANTA: Google ya bayyana jihohi 10 na Najeriya da 'yan luwadi suka fi yawa a shekarar 2019

A lokacin ne suka tambayeshi ko zai so zuwa, sai yace bai taba zuwa Najeriya ba kuma ita ce kasar da yake son zuwa. Ya ce: "Ban taba zuwa Najeriya ba. Kuma nan nake son zuwa."

Ya kara da cewa zai so ziyarar kasar Egypt kafin daga baya a tambayeshi dalilinshi na son zuwa Najeriya a tattaunawar. Mawakin yace Najeriya waje ne mai cike da nishadi a rayuwa.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng