Sunaye: Kasar Saudiyya ta cire Najeriya daga cikin jerin kasashen da za ta dinga bawa VISA

Sunaye: Kasar Saudiyya ta cire Najeriya daga cikin jerin kasashen da za ta dinga bawa VISA

Duk da kullaliyar dangantaka dake tsakanin Najeriya da kasar Saudiyya, amma sai gashi a cikin sunayen da kasar ta fitar na kasashen da za ta dinga bawa mutanensu Visa idan sun isa kasar babu Najeriya a ciki

An ruwaito cewa kasar ta saki sunayen kasashen ne a jiya Juma'a 27 ga watan Satumbar nan, kwana hudu kenan bayan jakadan kasar Saudiyyar Adnan Mahmoud yayi magana akan cewar a shirye Saudiyya take da ta kara dankon zumunta da Najeriya.

Da yake sanar da sunayen kasashen guda 49, jakadan ya bayyana cewa masu yawan bude idon suna iya zama a kasar Saudiyyar ne na watanni uku kawai.

Haka kuma Najeriya da sauran kasashen da babu sunayen su a ciki, suna iya zuwa ofishin jakadancin kasar su nemi Visa a can.

KU KARANTA: Tashin hankali: Miji ya kone matarshi kurmus akan rikicin sayar da fili

Ga sunayen kasashen da zasu more da wannan garabasa ta karbar Visa idan sun shiga kasar ta Saudiyya:

1. USA

2. Canada

3. Kazakhstan

4. Singapore

5. Brunei

6. New Zealand

7. South Korea

8. Japan

9. Spain

10. Belgium

11. Malaysia

12. Austria

13. Cyprus

14. UK

15. Croatia

16. Estonia

17. Andorra

18. Denmark

19. Germany

20. Bulgaria

21. France

22. Hungary

23. Czech Republic

24. Holland

25. Italy

26. Finland

27. Ireland

28. Lithuania

29. Greece

30. Liechtenstein

31. Monaco

32. Iceland

33. Malta

34. Poland

35. Latvia

36. Norway

37. Russia

38. Luxembourg

39. Romania

40. Slovenia

41. Montenegro

42. Slovakia

43. Switzerland

44. Portugal

45. Sweden

46. Australia

47. San Marino

48. Ukraine

49. China

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng