Siyasar 2023: Hotunan takarar shugaban kasa na El-Rufai da Oshiomole sun bayyana

Siyasar 2023: Hotunan takarar shugaban kasa na El-Rufai da Oshiomole sun bayyana

A wani mataki mai daukan hankali, hotunan yakin neman zabe na takarar shugabancin kasar nan dauke da hoton shugaban jam’iyyar APC, Adams Oshiomole da gwamnan jahar Kaduna Malam Nasir Ahmad El-Rufai sun bayyana.

Jaridar Sahara Reporters ta bayyana cewa fastocin sun fara yawo a yanzu haka a jahar Legas, inda tace ta yi ido hudu da ire iren hotunan nan a unguwar Surulere ta jahar Legas, da kuma yankin dake kusa da dandalin wasa na jahar Legas.

KU KARANTA: Gungun yan bindiga sun bude ma kiristoci wuta a coci a Taraba, sun kashe mutane 3

Siyasar 2023: Hotunan takarar shugaban kasa na El-Rufai da Oshiomole sun bayyana
Hotunan takarar shugaban kasa na El-Rufai da Oshiomole sun bayyana
Asali: Facebook

Majiyar Legit.ng ta ruwaito a cikin wannan hoto dai an buga hoton shugaban APC, kuma tsohon gwamnan jahar Edo, Adams Aliyu Oshiomole da sunan dan takarar shugaban kasa a inuwar jam’iyyar APC, yayin da hoton Malam Nasiru El-Rufai yake dauke da sunan dan takarar mataimakin shugaban kasa.

Haka zalika wannan fasta yana dauke da wasu halaye guda 8 wadanda mabuga hotunan suka ce sune suka sanya mutanen biyu suka fi cancanta su tsaya takarar shugaban kasa da mataimaki a zaben 2023 domin gaji shugaban kasa Muhammadu Buhari.

Daga cikin wadannan halaye da mabuga fastocin suka buga akwai:

- Mutane biyu da suke da halin biyayya

- Mutane biyu da suke da mutunci

- Mutane biyu masu son zaman lafiya

- Mutane biyu da suka amince da Dimukradiyya

- Mutane biyu da suke da gaskiya da rikon amana

- Mutane biyu da suka yarda da sauya fasalin Najeriya

- Mutane biyu da basu yarda da siyasar ubangida ba

- Mutane biyu da suka yarda da hadin kan Najeriya

Daga karshe an rubuta sunan wata kungiya mai suna ‘Miyatti Allah Cattle Breeders Association’ a matsayin wadanda suka buga wadannan fastoci.

Dama dai masana siyasar Najeriya na has ashen gwamnan jahar Kaduna zai iya fitowa takarar shugaban kasa, amma bait aba tabbatar da haka a fili ba, kuma ko a yanzu bai ce komai game da wannan hoto ba.

Ku biyo mu a https://facebook.com/legitnghausa

ko a http://twitter.com/legitcomhausa

KU LATSA: Hanyar sauko da sabuwar manhajar jaridar Legit.com Hausa cikin sauki

Ga masu shawara ko korafi, a same mu a labaranhausa@corp.legit.com

Sanarwa na musamman: Shafin NAIJ Hausa ya koma Legit Hausa

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng