Yanzu Yanzu: Buhari na cikin ganawa da sarakunan arewa a Abuja

Yanzu Yanzu: Buhari na cikin ganawa da sarakunan arewa a Abuja

Shugaban kasa Muhammadu Buhari a ranar Juma’a, 23 ga watan Agusta ya gana da sarakunan gargajiya daga yankin Arewacin kasar.

An fara ganawan ne da misalin karfe 11:30 na safe a majalisar Fadar Shugaban kasa.

Daga cikin wadanda suka halarci taron akwai Sarkin Musulmi kuma Sultan na Sokoto, Alhaji Abubakar Sa’ad; Sarkin Kano, Muhammad Sanusi Lamido, Sarkin Bida, Etsu Yahaya Abubakar da kuma Sarkin Daura.

Har yanzu ana kan gudanar da taron a daidai lokacin kawo wannan rahoton.

Ga hotunan haduwarsu a kasa:

Yanzu Yanzu: Buhari na cikin ganawa da sarakunan arewa a Abuja
Shugaba Buhari tare da sarakunan arewa a Abuja
Asali: Twitter

Yanzu Yanzu: Buhari na cikin ganawa da sarakunan arewa a Abuja
Buhari ya ganawa da sarakunan arewa a Abuja
Asali: Twitter

Yanzu Yanzu: Buhari na cikin ganawa da sarakunan arewa a Abuja
Buhari tare da Sarki Sanusi
Asali: Twitter

KU KARANTA KUMA: Babban magana: Magoya bayan Uche Nwosu sun lakada wa jami’an DSS dukan tsiya

A wani labarin kuma, Legit.ng ta rahoto a baya cewa Gwamnatin tarayya da gamayyar kungiyar ‘yan kwadago za su zauna domin kai karshe a kan maganar mafi karancin albashin ma’aikata ranar Juma’a 23 ga Agusta.

Jaridar The Nation ta ruwaito cewa ana sa ran za a cinma matsaya guda wadda kuma za ta kasance ta karshe bayan wannan ganawar.

Ministan kwadago Sanata Chris Ngige ya shaidawa manema labarai a ranar Laraba cewa maganar mafi karancin albashi ita ce kan gaba a cikin ayyukan da zai soma yi da zarar ya shiga ofis.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng