Takaitaccen tarihin ministan shari'a na Najeriya, Abubakar Malami SAN

Takaitaccen tarihin ministan shari'a na Najeriya, Abubakar Malami SAN

An haifi ministan shari'a na Najeriya kuma lauyan koli na kasa na yanzu, Abubakar Malami, a ranar 17 ga watan Afrilun shekarar 1967 a karamar hukumar Birnin Kebbi wadda ta kasance babban birnin jihar Kebbi.

Ya fara karatunsa na zamani a mataki na farko a makarantar Nassarawa Firamare da ke Birnin Kebbi kafin ya wuce College of Arts and Arabic Studies inda ya kammala karatunsa na Sakandire.

Malami ya kammala karatunsa na digiri a jami'ar Usman Danfodio a shekarar 1991 a fannin nazarin shari'a inda ya samu kwarewa ta zama lauya a shekarar 1992.

A shekarar 1994 ne Malami ya yi karatun digiri na biyu a jami'ar Maiduguri a fannin nazarin kula da kuma shugabancin al'umma wato Public Administration.

Kasancewarsa kwararren lauya, Malami ya yi aiki a matsayin lauyan kuma majistire a jihar Kebbi, hakazalika ya kasance mashawarcin a kan harkokin shari'a ga tsohuwar jam'iyyar CPC ta kasa, Congress for Progressive Change.

Ya samu karin girma inda ya zamto babban lauyan kasa wato SAN (Senior Advocate of Nigeria) a shekarar 2008.

Malami ya bayar da gudunmuwa mai yawan gaske wajen kafa jam'iyyar APC a shekarar 2013, inda ya kasance cikin sahun wadanda suka shiga kuma suka fita a gwagwarmayar da aka yi ta hade tsaffin jam'iyyun CPC da kuma ANPP, All Nigeria Peoples Party.

A shekarar 2014, Malami ya yi takarar gwamnan jihar Kebbi a karkashin inuwa ta jam'iyyar APC, inda ya sha kayi a hannun gwamna Abubakar Atiku Bagudu yayin zaben fidda gwanin takara.

KARANTA KUMA: Ngige, Malami da sauran ministoci 10 da zasu maimaita mukamansu a zango na biyu

Bayan samun nasarar shugaban kasa Muhammadu Buhari a babban zaben kasa na 2015, ya nada Malami a matsayin Ministan Shari'a kuma Lauyan kolu na kasa.

Nadin mukamin da Malami ya samu a ranar 11 ga watan Nuwamban 2015, ya sanya ya kasance mafi kankanta ta fuskar shekaru a cikin jerin 'yan majalisar zantarwa ta gwamnatin Buhari.

Bayan lashe zabensa a wa'adi na biyu da aka gudanar a bana, shugaban kasa Buhari a ranar Laraba 21 ga watan Agusta, ya rantsar da Malami a matsayin ministan shari'a kuma lauyan kolu na kasa karo biyu cikin jerin ministoci 43 da ya nada a sabuwar gwamnatinsa.

Sanarwa: Mun gode da kasancewarku tare damu yayin da shafin Naij.com Hausa ya sauya suna zuwa Legit.ng Hausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayarku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Domin shawara ko bukatar ba mu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.com

Ku biyo mu a shafukan mu na dandalin sada zumunta:

https://facebook.com/legitnghausa

https://twitter.com/legitnghausa

Asali: Legit.ng

Online view pixel