An kira mutum 80, 724 domin yin gwajin karshe na shiga aikin ‘Dan Sanda

An kira mutum 80, 724 domin yin gwajin karshe na shiga aikin ‘Dan Sanda

Mutane 80,724 ne sunayensu ya samu fitowa cikin wadanda za a dauka aikin ‘yan sanda a Najeriya. Daga ciki dai za a dauki mutum 10, 000 ne rak wannan aiki kamar yadda hukumar NPF ta bayyana.

Hukumar ‘yan sandan Najeriya za ta dauki mutane 10,000 ne a matsayin sababbin kuratan ‘yan sanda. Za a yi gwajin daukar aikin ne a karshen makon nan a ranar 3 ga Watan nan Agustan 2019.

‘Yan sandan kasar sun bayyana wannan ne ta bakin babban jami’in yada labarai da hulda da jama’a, Ikechukwu Ani. Ani ya fitar da wannan jawabi ne a Ranar Talata, 30 ga Watan Yuni, 2019.

Za a yi wannan gwaji ne a fadin jihohin kasar nan 36 da kuma babban birnin tarayya Abuja. Wannan ya na cikin manufar shugaba Muhammadu Buhari na bunkasa sha’anin tsaron kasar.

KU KARANTA: Za a baza na’urori CCTV a kan tituna saboda inganta tsaro a Najeriya

Kafin yanzu gwamnatin Buhari ta dauki wasu dubunnan a matsayin sababbin jami’an ‘yan sanda. Wannan zai sa a kama hanyar cike gurbin da a ke da su na karancin jami’an tsaro a Najeriya.

An samu fiye da mutane 315, 000 da ke neman shiga wannan aiki na ‘dan sanda. Da farko an zabi mutane 210, 150, daga baya a ka rage yawansu zuwa mutum 80, 724 da su ka kai matakin karshe.

Kakakin ‘yan sandan Najeriya ya bayyana cewa yanzu haka a na ta faman aikawa wadanda za su yi wannan jarrabawa ta karshe sakonni ta lambar wayoyinsu domin sanar da su game da shirin.

Za a fara wannan gwaji ne a Ranar Asabar mai zuwa da kimanin karfe 8:00 na safe. Hukumar za ta fitar da sunayen wadanda a ka zaba a manyan ofisisoshinta da ke ko ina a fadin Najeriya.

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewa tare da mu.

Ga masu bukatar manhajar mu na Azumi a wannan wata mai albarka sai a bibiyi wannan shafi https://fb.gg/play/ramadan_ramadan

Asali: Legit.ng

Online view pixel