Ganduje zai barnatar da dukiyar Talakawa a kan sababbin Sarakuna – Abba Yusuf

Ganduje zai barnatar da dukiyar Talakawa a kan sababbin Sarakuna – Abba Yusuf

Mun samu labari cewa Abba Kabir Yusuf ya fito yayi magana jiya 22 ga Watan Mayun 2019, a kan kacaccala Masarautun kasar Kano da gwamnatin jihar tayi a kwanan nan. Wannan ne karon farko da 'dan takarar na PDP yayi magana.

Injiniya Abba Kabir Yusuf ya bayyana cewa gwamna mai-ci Abdullahi Umar Ganduje ya saki layi wajen nada sababbin Sarakuna da yayi a jihar Kano da kuma sallamar Sakatarorin din-din-din daga aiki da kuma sukar Malaman addini.

‘Dan takarar gwamnan na PDP a zaben da ya gabata ya bayyana cewa wadannan matakai da gwamnatin Kano ta ke dauka ba shi ne abin da al’umma su ke bukata a yanzu ba. Yusuf ya bayyana wannan ne wajen wani taron buda-baki.

KU KARANTA: Ganduje ya ba Sarkin Kano Muhammad Sanusi II wasu zabi 3

Ganduje zai barnatar da dukiyar Talakawa a kan sababbin Sarakuna – Abba Yusuf
Abba Yusuf yace ilmi ya kamata a gyara ba nada Sarakuna ba
Asali: Facebook

‘Dan takarar yake cewa sun samu labari cewa za a kashe daruruwan miliyoyi wajen gina fadar Sarakunan da kuma sayewa Sarakunan da ya nada motoci na kasaita a daidai lokacin da ake fama da mutane su na neman abinci da matsuguni.

Haka zalika a jawabin da ‘dan takarar yayi, yace Kano na fama da yara fiye da miliyan 3 da ba su zuwa makarantar boko da kuma matasa miliyan 4 da ba su da abin yi da tarin Almajirai, amma Ganduje ya dage da kirkirar wasu Sarakuna 5 a jihar..

Yusuf ta bakin Sanusi Bature Dawakin/Tofa ya bayyana cewa ba za su yarda da abin da zai raba kan jama’ar Kano da tarihi ba inda yayi farin ciki da kotu ta dakatar da shirin gwamnan. A karshe yayi kira ga jama’a su dage da addu’a a wannan Wata.

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewa tare da mu.

Ga masu bukatar manhajar mu na Azumi a wannan wata mai albarka sai a bibiyi wannan shafi https://fb.gg/play/ramadan_ramadan

Asali: Legit.ng

Online view pixel